2015/09/04

HUDUBAR JUMA A DAGA MASALLACIN MANZON ALLAH 20 11 1436h TA SHEIKH SALAH ALBUDAIR











HUXUBAR MASALLACIN ANNABI (r)
JUMA'A, 20 /ZUL QI'IDAH/1436H




LIMAMI MAI HUXUBA
SHEHI SALAH ALBUDAIR







TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
بسم الله الرحمن الرحيم
HUXUBAR FARKO
Yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya haskaka basirar muminai da shari'arSa,      Ya kuma bayyana halal daga haram ga mukallafai (masu hankali, baligai),    Kuma ina shaidawa babu abun bautawa da gaskiya sai Allah; shi kaxai ya ke, bashi da abokin tarayya, kuma bashi da mai taimako.
Kuma ina shaidawa lallai annabinmu kuma shugabanmu annabi Muhammadu bawan Allah ne kuma manzonSa; da ya bayyanar da hukunce-hukunce, da qa'idodin musulunci ga masu bi; sannan yace:
"Wanda Allah yake nufinsa da alkhairi ya kan fahimtar da shi addini".
Salatin Allah da sallamarSa su qara tabbata a gare shi, da iyalansa da sahabbansa; khalifofin addini, waxanda suka cika da yakini.

            Bayan haka;
           
Ya ku musulmai …
Ku kiyaye dokokin Allah,    saboda taqawar Allah itace mafificin aiki,    Yi masa xa'a kuma shine mafi xaukakar nasaba, ko danganta;
"Ya ku waxanda suka yi imani ku kiyaye dokokin Allah iya kiyayewa, kuma kada ku mutu face kuna musulmai",  [Ali-imraan: 102].

            Ya ku musulmai …
Aikin hajji xaya ne daga cikin rukunnai guda biyar waxanda aka gina musulunci akansu,            Kuma yana wajaba akan balagagge mai hankali (mukallafi) da yake da iko, sau xaya a rayuwa.

Kuma duk wanda hajji ya wajaba akansa, kuma yake da ikon aikata shi   =  To dole ne a kansa ya gaggauta aiwatar da shi;          Ya zo daga Abdullahu xan Abbas    (رضي الله عنهما) yace:     Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Duk wanda ya nufi aikin hajji to ya gaggauta shi;       saboda rashin lafiya ka iya bijirowa,       ko hanya ta gurvace,      ko wata buqatar ta bijiro".     Ahmad da Ibnu-Majah suka ruwaito shi.

            Wanda kuma ya mutu gabanin ya sauke farillar hajji,     sawa'un yayi sakaci cikin hakan, ko bai yi sakaci ba,      kuma daidai ne yayi wasicin cewa a yi hajjin a gare shi ko bai yi wasici ba   =   To sai a fitar da kimanin abinda zai yi masa hajji da umrah daga cikin abinda ya bari na dukiya;         Saboda hadisin Abdullahi xan Abbas  (رضي الله عنهما) Lallai wata mata daga qabilar juhaina ta zo wajen Manzon Annabi (صلى الله عليه وسلم) sai tace: Lallai uwata tayi bakancen zata yi aikin hajji, sai bata samu ta yi hajjin ba, hart a mutu; Shin zan mata hajjin?       Sai yace: Na'am kiyi mata hajji;    Shin idan akwai bashi akan mamarki; zaki biya mata?     Ku biya Allah bashinSa;     saboda Allah shi yafi cancantar a biya shi". Bukhariy ne ya ruwaito shi.

            Wanda kuma ya samu ikon yin hajji da kansa to bai halatta ya wakilta wani mutum ya yi hajjin a gare shi ba.

            Wanda kuma sharuxan wajabcin hajji suka tabbata akansa,          Sai kuma ya gaza yinsa da jikinsa;      saboda wani uzurin da aka xebe tsammanin gushewarsa;     kamar gurguntaka da cutar da ta jima, ko dai wani rashin lafiyar da ba a tsammanin warkewarsa, ko kuma ya kasance ba zai iya tabbata akan abun hawa ba; sai da matsananciyar wahalar da ba za a iya jure mata ba,    ko kuma ya kasance tsofo ne da qarfinsa ya qare     =   To wajibi ne akansa ya samar da wanda zai yi hajji da umrah a gare shi;           Ya zo daga Abdullahi xan Abbas (رضي الله عنهما) lallai wata mata tace:         Ya ma'aikin Allah!       Lallai farillar Allah akan bayinsa na hajji ta riski babana yana dattijo mai yawan shekaru;      Ba zai iya tabbata akan abin hawa ba;      Shin zan iya yin hajji a gare shi?      Sai yace:     E; na'am".      Bukhariy da Muslim suka ruwaito shi.

            Kuma duk lokacin da mutum ya wakilta wani yayi masa aikin hajji,     sa'annan sai ya samu lafiya   =  To ba wajibi ba ne akansa ya yi wani hajjin na daban;    saboda ya aikata abinda aka umurce shi da shi;    sai ya fita daga zargi.

            Shi kuma wanda yake fatan zai samu ikon yin hajji da kansa,     ko kuma ana tsammanin gushewar cutarsa,    to lallai baya halatta a gare shi ya wakilta wanda zai yi hajji a gare shi;     Idan kuma ya aikata haka    to bai isar masa ba.

            Shi kuma faqirin da bashi da kuxin aikin hajji to hajjin baya wajaba akansa,     kuma ba zai nemi wani ya wakilce shi ba,      haka ba za a yi masa hajjin ba.     Saidai babu laifi; Wani ya bashi kuxin hajjin.

            Wanda kuma aka biya masa kuxin hajji,     sai kuma ya zama baya tsoron idan ya karva za a yi masa gori, ko a cutar da shi,  to babu laifi ya karva; yayi hajjinsa da shi.

            Kuma wanda bai yi hajjin musulunci na wajibi ba to bashi da damar yayi hajji ga waninsa;     Idan kuma ya aikata hakan to hajjin ya zama nasa;      wannan kuma saboda hadisin Abdullahi xan Abbas (رضي الله عنهما) lallai Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yaji wani mutum yana cewa:     Ya Allah na amsa maka zan yi hajji wa Shubruma, Sai Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Wanene Shubruma? Sai yace: Dangina ne makusanci. Sai yace: Shin ka tava yin hajji?   Sai yace: A'a!  Sai yace:  Ka mayar da wannan ta zama taka,   Sa'annan daga baya kayi hajji wa Shubrumah".    Ahmad da Abu-dawud da Ibnu-Majah suka ruwaito shi.

            Halal ne mutum ya karvi wani lada, idan ya wakilci wani cikin hajji.
Saidai abinda yafi ga mai wakiltar waninsa shine ya karbi kuxin da zai biya buqatunsa na hajji,  amma kada ya karvi lada.

            Yin haramar hajji ga mutane guda biyu baya qulluwa;   Don haka duk wanda yayi haramar hajji xaya ga mutane guda biyu, ko kuma ga kansa da waninsa   =  to haramarsa ta auku ne wa kansa kaxai.       Idan kuma ya yi haramar yin umrah ga wani, sannan yayi aiyukanta har ya kammala.       Sa'annan yayi haramar aikin hajji ga wani mutum na daban    to hakan ya inganta;    saboda a wannan yanayin ibadodi guda biyu ya aikata.

             Kuma mustahabbi ne mutum yayi hajji ga iyayensa guda biyu;    in dukkansu sun mutu,    ko kuma sun gajiya;     Amma sai ya fara yin hajjin wa mahaifiyarsa;  kasancewar itace abar gabatarwa cikin biyayyarsa.     Saidai kuma zai gabatar da hajjin da zai yi wa mahaifinsa na wajibi, akan wanda zai yi wa mahaifiyarsa na nafila.

            Kuma namiji bashi da haqqin ya hana matarsa yin hajjin musulunci (na wajibi);  matuqar ta samu muharrami;     Kuma muharrami ga mace yana daga ikonta na hajji.
Saidai kuma Imamu Maliki (رحمه الله) yace:   Mace zata iya fita hajji cikin taron mata ko tawagarsu.

            Duk kuma matar da mijinta ya mutu to baza ta fita zuwa ga hajji ba a cikin kwanakin iddar mutuwa;   saboda idda lokacinta yana qarewa, shi kuma hajji lokacinsa baya qarewa.       Kuma idan labarin rasuwarsa ya iske ta;   alhalin bata yi nisa daga gida ba   to sai ta dawo; don tayi iddarta a gidanta.       Idan kuma tayi nisa to sai ta cigaba da tafiyarta.

            Kuma duk wanda akansa akwai bashin da wajibi ne ya biya shi; saboda shigar lokacin biyan    to sai ya gabatar da shi akan hajji;        Saidai idan mai bashin yayi masa izinin tafiya hajji.      Wanda kuma bashinsa ya zama biyansa kucul-kucul ne,  kuma ya zama ya mallaki kason kowani lokaci; wanda zai biya idan lokacinsa yayi to sai ya tafi hajjinsa, ba tare da an sharxanta neman izinin wanda yake bin bashin ba.

            Ya ku musulmai …
            Barin yin hajjin nafila, ko umrah ta nafila a lokacin tsananin cunkoson jama'a     da nufin yalwatwa masu rauni da mata da marasa lafiya da tsofaffi masu yawan shekaru; waxanda suka zo don sauke hajjin farilla    =    barin haka shine yafi kusa da xa'a da alheri da samun lada da sakayya a wurin Allah;     Saboda yin hajjin nafila, da umrah ta nafila sunnah ne,      yayin da qoqarin kiyaye cutar da musulmi kuma wajibi ne;           Ya zo daga Abdurrahman xan Auf (رضي الله عنه) yace:     Annabi (صلى الله عليه وسلم) yace da ni:    
"Yaya ka aikata lokacin tava hajarul aswad?      Sai nace:    Na kan tava,       Na kan bari.     Sai yace:     Ka aikata daidai".   Ibnu-hibbana ne ya ruwaito shi.
Ma'anan wannan shine: Ya tava a lokacin da babu cunkoso,      ya kuma bar tava dutsen a yanayi na cunkoso,    Sai Annabi (صلى الله عليه وسلم) ya bayyana cewa ya dace da shari'a.

            Bada sadaka shima yafi falala akan yin hajjin nafila, da umrah ta nafila;      idan har akwai danginsa da suke da buqata, ko kuma ana cikin wani zamani na yunwa,  ko kuma aka samu wassu daga cikin musulmai suna da matsananciyar buqatar sadakarsa, ko kuma buqatar ciyarwarsa;        Wata rana Abdullahi bn Almubarak ya fita zuwa ga hajji sai yaga wata budurwa tana xaukar maceccen tsuntsun da aka jefar da shi a bola,   Sai ya tambaye ta,     Sai tace: Ni da 'yar'uwata a wannan wurin bamu da abinci, sai abinda aka jefar a wannan bolar,    Sai Abdullahi ibnul Mubarak ya yi umurnin a mayar da raquman da suka yi lodin kayansa, ya kuma bata duka abinda ya ware don buqatar hajjinsa,     sa'annan yace: Yin haka shi yafi falala fiye da muyi hajji a wannan shekarar. Sa'annan ya koma garinsa.


            Ya ku musulmai…
            Duk wanda ba a bashi takardar izinin yin hajji ba, daga hukumomi     to wajibi ne ya jinkirta hajjinsa, a magana ingantacciya, har zuwa lokacin da zai samu izinin fita;    saboda maslahar shari'a ta hukunta iyakance adadin waxanda za su yi hajji da umrah;     domin tunkuxe matsalolin cunkoso da turarreniya,   da kuma hana yin aikin kara-zube.

            Ya ku waxanda kuke bin hanyar qarya, da algus, da wayo wa hukumomi ko mutane, da rashawa,      domin su guje wa dokokin da suka kawo tsari a aikin hajji      !!!

                 
            Ya waxanda kuke bin hanyoyi masu sarqaqiya, da hatsari;     domin ku gudu daga wuraren 'yan sandan kan hanya masu kula da aminci; waxanda ba a sanya su a wuraren aikinsu ba sai don maslahar hajji da samun aminci a cikinsa, da kuma don samun lafiyar mahajjata  !!!


            Ya ku waxanda kuke sava wa shari'a, kuke kuma qetare dokokin Allah (تعالى), kuke aikata haram, sannan ku wuce miqaatai, da wuraren 'yan sanda ba tare da sanya ihrami ba  !!!

            Wani irin hajji kuke nufi ?!
Kuma wani lada kuke fatan samu?!

Alhalin kuma kuna yin qarya, da wayo, da sava wa dokoki !!!


Ya ku waxanda kuke tsallakar da waxanda suke sava wa dokoki, da kuma xauka ko tsallakar da waxanda suke nufin su yi hajji ba tare da sun haxa takardun izini ba   
Ku sani!   Ladan kwadagonku dukiya ce mai dauxa, kuma kuxi ne na haram, wanda aka samu ta hanyar savo!

Gabaxayanku!   
Ku hanu daga waxannan aiyukan abun zargi,     Sannan ku yi dubi zuwa ga al'amuran da idanu na hankalta, da hikima, da kuma qoqarin sauke nauyi.

Kuma ku nisanci kafa hujja da hujjoji rusassu; waxanda suka fi gidan sauro sakwarkwacewa idan za a tattauna akansu,    irin hujjojin da suke sanya wanda ya yi riqo da su a wajen tattaunawa dalilansa su qare yayi shiru ya kasa wata magana   !!!

Ya Allah ka nuna mana shiriyarmu,
Ka kuma kare mu daga sharrin kayukanmu
Ya Mai karamci,      Ya Mai girma,    Ya Mai rahama!


HUXUBA TA BIYU
Yabo da godiya sun tabbata ga Allah;  wanda ya ilmantar da bayinSa, ya kuma sanar da su, sannan ya basu fiqihu a cikin addininsu ya fahimtar.
Kuma ina shaidawa babu abun bautawa da gaskiya sai Allah; shi kaxai yake bashi da abokin tarayya.
Kuma ina shaidawa lallai annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawansa ne, kuma manzonSa.
Allah yayi daxin salati da sallama a gare shi, da iyalansa da sahabbansa, da waxanda suka tafi akan turbar gaskiya, har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka:

Ya ku musulmai…
Ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku kula da su,   kuyi masa biyayya, kada ku sava masa, "Ya ku waxanda suka yi imani ku kiyaye dokokin Allah,   ku kasance tare da masu gaskiya",     [Taubah: 119].

Ya ku musulmai…
Ku lazimci sunnonin da suke da madogara,      waxanda malamai tabbatattu amintattu suka ruwaito su,      Sannan ku kiyaye bidi'oi da qirqirarrun al'amura,

Ka yi mamakin yawan waxanda suka tattaru akan bidi'oi,

Ko kuma suka karkace suka bar sunnoni, suka ware

Kuma ina suke da sunnah MUTANEN DA suka karkata zuwa ga kaburbura suna fatan samun alheri daga waxanda suke kwance a cikinsu ?!

Suka kuma fiskantar da zukatansu zuwa gare su, harma da fiskoki,

Suka riqi kabari abin dogaro, da wurin yaye bala'i,

Da mafaka,     da qofar samu,   da Katanga daga sharri,   da wurin fata !

Har suke sujjada akan qofofinsu,
Suke yanka abun yankansu a bakin qofofin,
Suke kuma yin xawafi da kewaya kaburburan,

Wai !!! suna fatan samun yaye matsaloli daga gare su, da albarka, da kwararan alheri.

Bidi'oi masu girma da ake kiransu bautar kaburbura.

Wanda kuma tushensu shine bautar gumaka,

Jiga-jigan maluma masana, da shehunan musulunci duk sun yi ijma'i da ittifaqi,   kan cewa hakan yana cikin bidi'oi masu muni, waxanda suke cin karo ko warware musulunci da shari'ah.   Kamar su Abu-hanifata da Malik da Shafi'i da Ahmad.


Shi kuma Ubangijinmu Mai karamci yana kwararo kyauta,      yana kuma jin addu'ar bawa,     ba tare da masu ceto, ko wassu da za a riqa a matsayin tsani ba;    daga cikin annabawa ne ko daga cikin waliyyai.


Ku ziyarci masallacin Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم)… 
Kuna masu nisantar shafa katangun masallacin ko qofofinsa, da minbarinSa, da mihrabin sallarSa;    Domin ita albarka ba a nemanta cikin shashshafa daskararrun abubuwa.

Sannan ku nisanci neman albarka da qasar da take kan kaburbura,     ko neman waraka da ita,      ko kuma jejjefa abinci, da kwayoyi hatsi da kuxaxe akan kaburbura,      ko kuma roqon waxanda suke kwance a cikinsu;     saboda aikata hakan yana cikin aiyukan jahilai na jahiliyyah.


Aikinku Allah ya gama shi da karvuwa, da kuma bada lada,

Addu'arku kuma ya gama ta da yarda da kuma amsawa.

Ya kuma jawo muku arziqi, 
ya kuma bubbuxe muku qofofinsa.
 انتهت

Kuma kuyi salati ga Ahmad mai shiryarwa,
Mai kuma ceton mutane gabaxaya,

Saboda
Duk wanda yayi masa salati guda xaya
To lallai Allah zai yi masa guda goma,

Zuwa ga halittu aka turo shi, don ya zama rahama, mai tausasawa
Kuyi masa salati, da sallama masu tarin yawa;

Ya Allah kayi salati da sallama ga bawanka kuma annabinka Muhammad,
Kuma ya Allah ka yarda da dukkan iyalansa da sahabbai,
Ka haxa da mu, Ya Mai karamci, Ya Mai yawan baiwa,

Ya Allah ka xaukaka musulunci da musulmai,
Kuma ka qasqantar da shirka da mushirkai,
Kuma ka halaka azzalumai, da masu kasha bayinka, mavarnata, masu qetare iyaka,   Ya Ubangijin halittu!

Ya Allah ka tunkuxe yaquka da fitintinu da savani da rashin kwanciyar hankali, da jayayya    
daga qasashen musulmai gabaxaya,   Ya Mai karamci!

Ya Allah ka dawwamar wa qasarmu;  ta Saudiyya
Amincinta, da wadacinta, da xaukakarta, da kwanciyar hankalinta,
Kuma ka datar da shugabanninta zuwa ga abinda akwai alkhairi a cikinsa da gyaruwan musulmai,
Ya Allah ka datar da shugabanmu; Mai hidimar masallatai biyu; harami, maxaukaka,   da na'ibansa guda biyu
Zuwa ga abinda xaukakar muslunci yake cikinsa da gyaruwar musulmai,   Ya Ubangijin halittu!

Ya Allah ka warkar da marasa lafiya daga cikinmu,
Ka yaye ma waxanda aka jarrabe su daga cikinmu,
Kayi rahama ga mamata daga cikinmu,
Kuma ka fitar da waxanda suke cikin kurkuku,
Ka taimake akan wanda yayi adawa da mu,
Ya Ubangijin halittu!

Ya Allah ka kiyaye mahajjata,
Da masu ziyara, da masu umrah,

Ya Allah ka karvi aiyukansu
Kuma ka tsarkake musu, su
Ka kuma xaga darajarsu,
Ka xaukaka su,

Qarshen addu'armu ita ce:
ALHAMDU LILLAHI RABBIL ALAMINA !     

            

No comments:

Post a Comment

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...