2015/09/22

HUDUBAR IDIN LAYYAH DAGA MASALLACIN ANNABI 1436h na Assubaity








HUXUBAR LAYYAH DAGA MASALLACIN ANNABI (r)
ALHAMIS, 10/ZULHIJJAH/1436H




LIMAMI MAI HUXUBA
SHEHIN MALAMI ABDULBARIY XAN AWWADH AS-SUBAITIY







TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
بسم الله الرحمن الرحيم
Yabo na Allah ne;    yabo mai yawa, mai daxi, mai albarka, madawwami; da dawwamar izzarSa, da kuma kyan fiskarSa, da girman mulkinSa;    Muna gode masa maxaukakin sarki,     kuma shine wanda ya cancanci yabo da godiya.      Ba a iya qididdige ni'imarSa,    kuma ba za mu iya qididdige yabo a gare shi;        Saboda shi Allah kamar yadda yayi yabo ne wa kanSa.
Salati da sallama su qara tabbata ga bawanSa kuma mafi alheri cikin halittunSa,    salatin da adadinsa baya qarewa,      Wanda kuma bawan dake maimaita shi ba zai tava qoshi daga faxansa ba. 
ALLAHU AKBAR duk lokacin da mai azumi yayi azumi, sannan ya yi idi,       ALLAHU AKBAR duk lokacin da asuba tayi sannan gari ya waye,          ALLAHU AKBAR duk lokacin da mai hajji yayi aikin hajji, kuma yayi umrah,        ALLAHU AKBAR duk lokacin da shuka ya tsira sannan yayi fure,  ALLAHU AKBAR duk lokacin da ya bada wadaci ga wani bawa sannan ya talautar,  

A shekarar hajjin bankwana, a cikin yinin arfah mai girma, aya mai girma ta sauka;     wacce kuma itace mafi girman ni'ima ga wannan al'ummar;       [A yau na cika addininku a gare ku, kuma na cika ni'imata akanku, kuma na yarje muku musulunci addini] [Ma'idah: 3]
Kuma Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya rasu bayan tsayuwan arfah da kwanaki tamanin da xaya (91).
Kuma lallai Allah ya cika addini da Shi (صلى الله عليه وسلم);    don haka halittu basa buqatar wani addinin; wanda ba musulunci ba,    ko kuma wani Annabin wanda ba annabinsu ba (صلى الله عليه وسلم);    kuma shine cikamakon annabawa;      Babu abinda yake HALAL sai abinda ya halatta,    Babu kuma HARAM sai wanda ya haramta,    Babu kuma ADDINI sai abinda ya shar'anta,         Allah ta'alah yana cewa:
"Kuma kalmar Ubangijinka ta cika; gaskiya da adalci, Babu mai canza kalmominSa" [An'aam: ]. Wato; gaskiya cikin labarunSa, da kuma adalci cikin umurni da hani.
            Allah ya cika wannan addinin;     wannan yasa mutane basu da buqatar qarin wani abu (ko bidi'a) a cikin addini har abada;    Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Duk wanda ya qirqiro abinda babu shi a cikin addininmu wannan, to an mayar masa", Bukhariy da Muslim suka ruwaito shi.
Saboda haka; Babu wani alheri face Annabi ( صلى الله عليه وسلم) ya nuna shi wa al'ummarSa,      Haka babu wani sharri face ya tsawatar da al'ummarSa akansa.
            Allah ya yarje wa muminai wannan addinin;     don haka ba zai karvi wani addinin ba daga mutane in ba musulunci ba;   Allah ta'alah yana cewa:
"Duk wanda ya nemi wani addinin wanda ba musulunci ba, to baza a karva masa ba,     Kuma shi a lahira yana daga cikin masu hasara", [Ali-imraan: 85].
            [Musulunci shine] Addinin da ginshiqansa da qa'idodinsa da halayyansa suka cika,      kuma suka kai qololuwa wajen kamala,      Allah ta'alah yana cewa:
"Kace: Ya ku mutane lallai ni Manzon Allah ne zuwa gare ku, gabaxaya,   Wanda yake da mulkin sammai da qassai,  Babu abun bautawa face shi,   Yana rayawa yana kashewa" [A'araaf: 158].
            [Musulunci] Addini na har abada,      a mutanen duniya,     tabbatacce,   Wanda kuma shine miqaqqen tsarin rayuwa,      Kuma shine kammalalle;     duk kuma abinda aka samu na canje-canjen da zamani ya kawo,     ko yawan banbance-banbancen lokuta, (to addinin yana dacewa da su). Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Kuma duk wanda ya rayu daga cikinku to lallai zai ga savani dayawa;    Ina horonku kan riqo da sunnata da kuma sunnar halifofi shiryayyu masu shiryarwa,   Sai kuyi riqo da su,  kuma ku damqe su da fiqoqi,    Kuma ina muku kashedi kan qirqirarrun al'amura".  Ibnu-Hibbana ya ruwaito shi a cikin sahihinsa, da Alhakim a cikin almustadrak.
            Shari'ar musulunci itace mafi qarkon abinda za a jagoranci al'ummomi da ita,        Kuma itace tsarin da yafi maslaha;    wanda za a yi hukunci da shi a tsakanin mutane,    Tsari ne da ya dace da kowani zamani, da kuma kowani wuri,    da kuma kowace al'umma,     da kuma kowani hali,      Kai, yadda lamarin yake shine:     Duniya baza ta tava gyaruwa da wani tsarin wanda ba na musulunci ba.     Kuma duk lokacin da zamani ya qara nisa,        al'ummomi suka qara samun bunqasa      sai wassu dalilai saabi su sake bayyana kan ingancin musulunci,    da kuma xaukakar sha'aninsa.
            Kuma yana daga cikin kamalar musulunci kasancewarsa abu ne guda;   wanda baya vantaruwa,     kuma abu ne dunqulalle baya rarraba,       Allah ta'alah yana cewa:
"Ya ku waxanda suka yi imani ku shiga musulunci gabaxayansa" [Baqarah: 208].
            Baka samun tufka da warwara cikin hukunce-hukuncen addinin musulunci,   kuma baka samun banbance-banbance cikin shari'arsa,      Allah ta'alah yana cewa:
"Kuma da (Alqur'ani) ya kasance daga wajen wani wanda ba Allah ba, to da sun samu savani dayawa a cikinsa" [Nisa'i:  82].
            Kuma lallai waxanda basa gudanar da rayuwarsu a qarqashin tsarin Allah,      Sai suke hukuntar da wassu tsare-tsare akansu; waxanda mutane suka samar da su,     Irin waxannan suna cin karo da tsarin rayuwa,      kuma lallai rayukansu baza su samu nitsuwa ba,     kuma fixirarsu baza ta daidaita ba,    sannan baza su ji daxin rayuwarsu ba,     Kuma lallai aikata hakan zai bayyanar da munanan alamomi masu halakarwa masu rushe rayuwa.

            Amma shi kuma musulunci;        To tsari ne na rayuwa cikakke,      Wanda yake tsara alaqar mutum da xan'uwansa mutum,       da kuma alaqar mutum da duniyar; da take kewaye da shi,        kuma musulunci yana biyan dukkan buqatun 'yan adam,     a lamuran duniya dana lahira,      a halin zaman lafiya dana yaqi,   a lamarin siyasa dana tattalin arziqi,      Allah ta'alah yana cewa:
"Kuma mun sassaukar da wannan littafin akanka don ya zama bayani ne ga kowani abu, kuma shiriya da rahama da albishir ga musulmai" [Nahli: 89].
            Kuma musulunci shari'a ne na Ubangiji,     wanda yake gyara abubuwa na zahiri,    kuma yake bada tarbiyya ga na baxini,     kuma babu wani aibi a cikinsa,    kuma baya bin ganin dacewar halittu, ko son ransu ko maslahar da suke gani,  ko duk abinda yake ingizo xaixaikunsu,        Yayin da su kuma dokokin da halittu suke tsarawa ko su sanya   koda sun iya magance abubuwa na zahiri,   to lallai baza su iya magance matsalolin zukata ba,        Su dokokin da halittu suke sanyawa suna xauke ne da baji ko taake na qarya,    Wanda kuma baza                                          su iya kawo wa 'yan adam zaman lafiya ko aminci ba.
            Kuma lallai za a iya samun nasarori na wucin gadi a xan wani lokaci  ga wanda ya riqi sabbuban cin nasara,    Saidai kuma nasara ce mai tawaya wacce baza ta xore ba,     kuma sharri da matsaloli zasu dabaibaye nasarar,    kuma amincin da za a iya samu ba zai zama cikakke ba; cikin waxanan tsare-tsaren, tare da samun qarancin albarka cikin arziqi da 'ya'ya,    Allah ta'alah yana cewa:
"Kuma duk wanda ya kawar da kai ga ambatona to lallai yana da rayuwa ta qunci,   kuma zamu tayar da shi a qiyama makaho" [Xaha:  124].
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, LA ILAHA ILLAL LAHU, ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, WA LILLAHIL HAMDU.
Addininmu yana kiyaye hankulan mutane;   a don haka,  ya haramta shan giya, da dukkan abubuwa masu bugarwa,    ko duk abinda zai lalata hankali.
Kuma addinin ya kiyaye dukiyoyi;  shi yasa ya kwaxaitar kan riqe amana, ya kuma haramta yin sata.
Kuma addininmu yana kiyaye rayuka;     wannan yasa ya haramta kashe rayuka ba tare da haqqi ba.
Kuma addininmu yana kiyaye lafiyar jiki;   shi yasa ya Allah yake cewa:
"Kuma, ku ci, ku sha, kada kuyi varna;    lallai shi baya son mavarnata" [A'araaf:   31]. 
Kuma musulunci ya haramta alfasha; abinda ya bayyana daga cikinta, da abinda ya vuya.
            Kuma addininmu yana bada kariya wa alaqoqi, da tsarin dangantaka;     ta hanyar tsarin aure da iyalai,     kuma yana kiyaye xaukakar xan'adam da karamarsa;      Baya barin sha'awa ta tafi kara zube; ba tsari;     Wannan yasa musulunci ya bada kariya wa hanyar samun 'ya'ya,      ya kuma katange mace,      sannan ya sanya tubalin da za a gina samar da iyalai,     wannan kuma domin su tsira, tsira mai kyau,       kuma su bada 'ya'ya masu albarka,     Allah ta'alah yana cewa:
"Yana daga cikin ayoyinSa; Ya halitta muku mata daga kayukanku domin ku nitsu zuwa gare su, kuma ya sanya qauna da tausayi a tsakaninku,    Lallai cikin haka akwai abin lura ga mutane masu tunani" [Ruum: 21].
            Addinin adalci tare da baqo, da kuma aboki,      da      na nesa harma da maqiyi,     Allah ta'alah yana cewa:
"Kuma idan zaku yi zance kuyi adalci, koda ya kasance ma'abucin kusanci" [An'aam: 152].   Ya kuma ce:
"Kuma kada qiyayyar wassu mutane ta hana ku yin adalci;   kuyi adalci shi yafi kusa da bin dokokin Allah" [Ma'idah: 2].
            Addinin qarfi da kwazo da aiki da azama,     Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Mumini mai qarfi shi yafi alkhairi kuma shi yafi soyuwa a wurin Allah akan mumini mai rauni,     tare da cewa Kowanne yana da alkhairi,     Kayi kwaxayin aikata abinda zai  amfanar da kai,    sai ka nemi taimakon Allah,     kada ka gajiya". Muslim ne ya ruwaito shi.

            Musulunci yana kira zuwa ga xinke zukata,   da daidaita sahun musulmai,      kuma shine addinin soyayya da haxin kai, da tarayya da tausayi ko rahama,      Allah ta'alah yana cewa:
"Kuma ku tuna ni'imar Allah akanku a yayin da kuka kasance maqiya sai ya daidaita tsakanin zukatanku;     sai kuka wayi gari da ni'imarsa kuna 'yan'uwa" [Ali-imraana: 103].
Kuma lallai idi ya kan zo don ya qara jaddada waxannan ma'anonin,   ya kuma qara qarfafa dangantaka, da alaqoqi.

            Kuma lallai al'ummar musulmai suna fatan wannan ni'imar (wato: ni'imar haxin kai) ta lulluve qasar YEMEN mai albarka,     YAMEN garin imani da hikima (kamar yadda Annabi ya shaidar),      Har waxanda suka yi fito-na-fito da shugabanni su koma cikin hankulansu da shiriyarsu,     Wato su miqa wuya ga kiran dake cewa: Suyi amfani da hankulansu,      don tsayar da zubar da jini,     da bada kariya ga rayukan da ake ta kashe su,   da kuma  kiyaye lalata dukiyar da aka yi wahala taquru wajen samar da ita,     Allah ta'alah yana cewa:
"Kuma kada kuyi jayayya sai ku yi rauni, sai qarfinku ya tafi" [Anfaal: 46].
Kuma lallai Annabi (صلى الله عليه وسلم) yana xaukar fito-na-fito da jama'ar musulmai da kuma rabuwa da su a matsayin ridda irin ta jahiliyyah,      A inda yace:
"Kuma duk wanda ya fice daga biyayya, ya kuma rabu da jama'a, sai ya mutu; to yayi mutuwa irin ta jahiliyyah", Muslim ya ruwaito shi.

            Addininmu yana karantar da mu cewa; Lallai IMANI SHINE sababin samun aminci (a cikin al'ummai),     kuma shine sababin kiyaye tabbatuwansa;     "Kuma su bautawa Ubangijin wannan xakin;    Wanda ya ciyar da su daga yunwa,    Ya kuma amintar da su daga tsoro" [quraish: 3-4].
Irin wannan amincin da muke rayuwa a cikinsa a qasarmu, muke kuma hutawa a qarqashin inuwarsa,     Ni'ima ce da baza a iya misalta girmanta ba,     kuma baiwa ce daga Allah wacce ba za a iya gama siffantata ba,           AMINCI SUMFUXAXXE CIKAKKE GAMAMME,      Wanda ya bada dama wa kowa-da-kowa (jam'i mai albarka) wajen sauke hajjinsu cikin sauqi,     nitsuwa ta kewaye su,    kwanciyar hankali ya lulluve su,          Su kuma abubuwan da ka iya aukuwa; su wuce     to lallai basa qaranta qimar qoqarin da aka yi, da dukiyoyin da aka kashe,   da nasarorin da aka cimma;   waxanda idonuwan mutum adali baza su kuskure musu ba.
         
            Kuma lallai muna jin baqin ciki da vacin rai da takaici, kan rashin aminci a qasar SIRIA mai izza;     Haqiqa yanayin wannan qasa ya canza,    rayuwa ta gurvace,    an qaurace wa gidaje;    mutane dayawa sun qaura sun bar qasarsu,     An kakkashe rayukan da basu-ji- ko suka-gani-ba,   Wassu yaran an mayar da su marayu,      wassu matan kuma zawarawa!
            Muna roqon Allah da sunayensa da sifofinsa, ya tabbatar da gaskiya, ya kuma ruguza varna,  kuma ya yaye baqin cikin waxanda aka mayar da su masu rauni (da gangan),   ya kuma kawar da baqin cikin masu neman mafaka,   ya mayar da su gidajensu suna kuvutattu,   ya mayar da makircin maqiyansu zuwa ga qirazansu.

            MASALLACIN QUDUS shima yanayinsa yana ta kokawa   saboda rashin aminci,    kasancewar an kekketa alfarmarsa,  kuma masu varna sun yi aikinsu na varna a mafi yawancinsa.         Kuma wajibi ne akan musulmai;   su haxa hannu, suyi taimakakkeniya, tare da yin kururuwan cewa a taimaka masa, a kiyaye haqqinsa, da bada kariya wa iyakokinsa,  da kuma tsawatar ko yin horo ga masu yin ta'addanci a gare shi.       Kamar yadda muke miqa gaisuwa da jinjina, tare da qarfafa mazauna garin Qudus da 'yan'uwansu kan gwarzantakarsu, da matsaya da suka tsaya na nuna izza, da karama, da sadaukarwa;      don taimakon masallacin AQSAH, da kuma sauke wannan nauyi na wajibi.

            Musulunci ya sanya ILIMI da BUNQASA HANKALI don su zama ginshiqin gina al'umma da bunqasa ta, da kawo cigaba a gare ta,      Bai kuma sanya ilimi ya zama hanyar halakarwa ko rushe-rushe, ko ya dasa kwayoyin ta'addanci da yaxa zalunci, ko kuma bautar da al'ummomi da xan'adam ba.

            Kuma addininmu yayi fice wajen siffantuwa da tausasawa da kuma sauqi, kuma lallai tsanantawa da zafafawa baya cikin addini,   Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Lallai Allah ya wajabta kyautatawa ga kowani abu", Muslim ya ruwaito shi.
            Su kuma wawayen mutane masu qaiqasasshen zukata da wuce iyakar shari'ar Allah,     waxanda suke qone-qone a masallatai,    suke rurrushe gine-gine,     waxannan ba suna yin hakan ba ne a madadin musulunci ko kuma da yawunsa, Kai basu ma SAN haqiqanin musuluncin ba,  Kuma maqiyan musulunci sune suka shusshuka su a garurrukan musulmai, domin su munanawa sunan musulunci da sunan musuluncin,   kuma sune suke  jujjuya su ta qarqashin qasa,      bayan sun mori qarancin hankulansu,     da quntataccen tunaninsu;    ta hanyar sanya musu burin samun shugabanci da khalifanci,     da kuma tsayar da daular musulunci,     "Yana musu alkawari kuma yana sanya musu guri,    Amma ba komai Shexan yake alkawarta musu ba face ruxi" [Nisa'i: 120].

            Kuma addininmu yana kiran mutane zuwa aiki da mafi kyan halayya, da aiyuka,      Allah ta'alah yana cewa:
"Ka tunkuxe (cutarwar da aka yi a gare ka) da abinda yafi kyau, Sai wanda a tsakaninka da tsakaninsa akwai adawa ya zama kamar majivincin makusanci" [Fussilat: 34].

            Addininmu yana umurni da rufa asirin mutane,     da biyan buqatar musulmai,       da yaye musu baqin cikinsu,     da ziyartar marasa lafiya,     da rakiyar gawa,      kuma yana umurni da cewa bawa ya so wa xan'uwansa irin abinda yake so wa kansa.

            Kuma addininmu yana yin umurni kan biyayya wa iyaye,     da kyautata mu'amala ga miji da 'ya'ya,    da sadar da zumunci,  da karrama makwabci,    da tausasawa dabbobi,    Allah ta'alah yana cewa:
"Lallai Allah yana yin umurni da yin adalci, da kyautatawa, da yin baiwa ga ma'abota kusanci,    kuma yana hana alfasha da munkari, da zalunci,  Yana muku wa'azi da fatan zaku wa'aztu" [Nahli: 89].

            Allah ya yi albarka a gare ni, da ku, cikin alqur'ani mai girma.  Ina faxar wannan maganar, kuma ina neman gafarar Allah wa Ni da Ku;       sai ku nemi gafararSa;   lallai shi mai gafara ne, mai rahama.

HUXUBA TA BIYU
            Yabo ya tabbata ga Allah wanda ya halicce mu cikin mafi kyan tsari,      Ya kuma sanya asalinmu (babanmu Annabi Adamu) ya zama daga turvaya,        Ina yin godiya a gare shi kuma ina yaba masa;     shine wanda ya karrama muminai da aikinsu,    ya kuma sanya aiyukan kafirai ya zama watsettse abun sheqewa,      Kuma ina shaidawa babu abun bautawa da gaskiya sai Allah;    zuwa gare shi makoma take.
            Kuma ina shaidawa lallai annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawanSa ne manzonSa;      wanda yayi hani kan gibar mutum da annamimanci, da zage-zage.
            Allah yayi daxin salati a gare shi, da iyalansa da sahabbansa;     salatin da zai dawwama har zuwa ranar hisabi.
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, LA ILAHA ILLAL LAHU, ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, WA LILLAHIL HAMDU.

Duniya –Ya ku bayin Allah- a cikinta ake shuka abinda za a girbe a lahira,   Sai ku yi guzuri daga duniyarku ga lahirarku, da kyawawan aiyuka,     Saboda a yau duniya aiki ake yi babu hisabi,     Gobe kuma qiyama hisabi ne babu aiki.
            Lallai yininku wannan yini ne mai girma;    wato: Yinin hajji babba,       Kuma a cikin wannan yinin ne; mahajjata da waxanda ba mahajjatan ba; Suke yin tarayya  wajen zubar da jinin hadaya da layyah a cikinsa,    suna masu kusantar Allah mabuwayi da xaukaka da aikata hakan, Allah ta'alah yana cewa:
"Naman dabbobinku baya samun Allah, haka jinanensu,    Saidai bin dokokin Allah wanda yake tare da ku shine yake samunSa" [Hajj: 37].
            Kuma baya halatta ayi layyah da dabba ramammiya, da maras lafiya, da gurguwa, da mai ido xaya, da makauniya, da wacce ta samu karaya, ko kuma dabbar da qahonta ya tafi, ko mafi yawan kunnenta.     Kuma raqumin da yake xauke da cutar quraje masu yaxuwa shima baya isarwa a layyah.
            Kuma daga cikin raquma basa isarwa sai wanda ya cika shekaru biyar (05) ko fiye,      Daga cikin shanu kuma sai wanda ya cika shekaru biyu (02),    Daga cikin awaki kuma sai wanda ya cika shekara guda (01),      Daga cikin tumaki kuma sai wanda ya cika watanni shida (6).
            Kuma raqumi xaya ya kan isar wa mutane bakwai (7),  Haka itama saniya ta kan isar wa mutane bakwai (7), Ita kuma akuya ga mutum xaya da mutanen gidansa.
            Kuma ba zai sayar da wani abu na daga jikin dabbar layyarsa ba,    kuma ba zai baiwa mahauci ladan wahalarsa daga dabbar layyarsa ba.
            Kuma lokacin yankan layya yana farawa ne daga bayan sallar idi, har zuwa faxuwar ranar yinin goma sha uku (13), daga cikin kwanakin da ake shanya nama don busar da shi.
            Shi kuma kabbara mai qayyadadden lokacin da ake yinsa bayan sallolin farillai: Yana farawa ne daga sallar asubar ranar arfah,        har zuwa sallar la'asar na yinin qarshe daga cikin kwanakin da ake shanya nama don busarwa.
            Ya ku musulmai !
            Kuyi bushasharku da idi,       ku sanya tufafi sabi,       kuma ku jaddada ma'anonin idi,       Kuna masu biyayya wa iyayenku,     da ziyartar makusantanku da 'yan'uwanku,       kuma ku bibiyi labarin makwabtanku,     kuma ku taimaki miskinai da faqirai da marayu,      Allah ya karva mana aiyukanmu na kwarai, da aiyukanku.    Kuma kowace shekara Allah ya sa kuna cikin alkhairi.

            Kuma kuyi salati wa fiyayyen halittun Allah; Muhammadu xan Abdullahi;       saboda Allah da Mala'ikunSa suna yin salati a gare shi;     
"Ya ku waxanda suka yi imani ku yi salati a gare shi;   da sallama mai yawa".
Ya Allah kayi salati wa Muhammadu da matanSa da zurriyarSa, kamar yadda kayi salati wa iyalan annabi Ibrahima. … 


       Huxubar ta qare,,,          ,,,          ,,,

No comments:

Post a Comment

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...