2015/09/27

AMSA WA UBANGIJI KIRANSA NA AYI HAJJI; DA KALMOMIN TAUHIDI (KADAITA ALLAH)







AMSA WA UBANGIJI KIRANSA NA AYI HAJJI;
DA KALMOMIN TAUHIDI (KADAITA ALLAH)
(التلبية بالتوحيد)





Na
Shehin malami
Prof. Abdurrazak bn Abdulmuhsin Albadr




Fassarar
Abubakar Hamza


Godiya ta tabbata ga Allah wanda shi ne abun yabo mai girma, Ina shaidawa babu abun bauta da gaskiya sai Allah shi kadai bashi da abokin tarayya shaidawar mutumin da ke tabbatar ma Allah tauhidinsa, wanda ke tsarkake shi ga barin abokin tarayya ko kishiya. Kuma ina shaidawa lallai annabi Muhammadu bawansa ne kuma manzonsa; ma'abocin falala da basa kirguwa da karamomi, tare da dukkan halaye abun yabo; Allah ya yi dadin salati da sallama a gare shi, da kuma iyalansa da sahabbansa gabadaya. Bayan haka;

Lallai farkon farin abin da musulmi zai bude aikin hajjinsa da shi na aiyuka shi ne: TALBIYYAH; fadin: LABBAIKAL LAHUMMA LABBAIKA … yana mai shelantawa –ta hanyar kalmomin talbiyyah masu girma- tauhidinsa ga Allahu (swt) shi kadai, tare da watsi da aikata shirka, ko sanya ma Allah kishiya. Sa'annan sai ya dauki hanyarsa ta tafiya dakin Allah 'yantacce, yana mai maimata wadannan kalmomi "LABBAIKAL LAHUMMA LABBAIKA, LABBAIKA LA SHARIKA LAKA LABBAIKA, INNAL HAMDA WAN NI'IMATA LAKA WAL MULKA LA SHARIKA LAKA" zai yi ta maimaita su yana mai sanin ma'anonin das u ke kunshe da su na tsantsanta aiki (ikhlasi) ga Allah, tare da kadaita shi (tauhidi), da kuma abin da su ka kunsa na wajabcin kadaita Allah shi kadai da bauta, tare da kuma nisantar rikon abokan tarayya tare da Allah. Zai rika fadin wadannan kalmomin yana mai halarto da su a cikin zuciyarsa, yana kuma tabbatarwa cewa lallai ubangijinsa (swt) shi ne ya kadaita da bada ni'imomi da kyautayi, babu wanda ke tarayya da shi cikin haka, kamar yadda shi kadai ya takaita da cancantar kadaitawar bayinsa, babu mai kishiyantarsa.

No comments:

Post a Comment

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...