2017/06/24

hudubar idi 1 SHAWWAL 1438H Ta Madina








HUXUBAR IDI
DAGA MASALLACIN ANNABI
(صلى الله عليه وسلم)
LAHDI,01/SHAWWAL/1438H







LIMAMI MAI HUXUBA
SHEHIN MALAMI DR. HUSAIN XAN ABDUL'AZIZ ALUS-SHAIKH




TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
IDI
     Shehin Malami wato: Husain xan Abdul'aziz Alus-Sheikh –Allah ya kiyaye shi- ya yi hudubar idin azumi na shekarar 1438H, mai taken: IDI, Wanda kuma ya tattauna a cikinta, akan Yadda idi yake a musulunci, da abinda yake tattare da su na walwala da bayyanar da farin ciki, da jin daxi, da annashwa, kuma a cikin huxubarsa ya bayyana wajabcin aiki da shari'a, da kuma komawa izuwa ga ma'abuta ilimi a lokacin matsaloli da fitintinu.


بسم الله الرحمن الرحيم
HUXUBAR FARKO
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, LA ILAHA ILLAL LAHU, WALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, WA LILLAHIL HAMD
Idi a musulunci yana xauke da manufofi maxaukaka, saboda a cikinsa ne musulmai ke farin cikin kammaluwar xa'arsu (ta azumi) ga Ubangijinsu, kuma su ke yin walwala ko nuna farin ciki; saboda buxa-bakinsu a bayan azuminsu, Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa: "Mai azumi yana da farin ciki iri biyu; farin ciki a lokacin buxa-bakinsa, da wani farin cikin a lokacin saduwarsa da UbangijinSa".
A cikin idi, akwai tuna manyan ginshiqai masu girma, wanda daga cikinsu, akwai, YADDA MUSULUNCI YA KWAXAITU WAJEN TABBATAR DA SOYAYYA A TSAKANIN MUSULMAI, DA KUMA HALIN QAUNA TSAKANIN MUMINAI, Allah (تعالى) yana cewa: "Kuma muminai maza da mata, sashensu majivinta sashe ne" [Tauba: 71],
Don haka, wajibi ne, mu riqi idi a matsayin sababin qarin sadar da zumunci, da qauna, kuma dama ta yin watsi da xabi'ar kyashi da qiyayya, Allah (تعالى) yana cewa: "Lallai ne muminai 'yan'uwana ne" [Hujurat: 10].
Kuma Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa: "Misalin muminai cikin soyayyarsu da qaunar junarsu, kamar misalin jiki ne guda xaya".
A lokacin idi, ana mana kiraye-kiraye da cewar mu riqa yaxa farin ciki, da shigar da shi ga rayuka, da kuma qarfafa ma'anonin rahama da jin-qai, da kyautatawa, da taimako.

Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya farlanta zakkar fid-da-kai, kuma ya ce: "Ku wadatar da faqirai, daga fita neman abinci, a yinin idi", Ad-daraquxniy ya rawaito shi.

'YAN'UWANA MUSULMAI…
Daga jerin qiyayyar maqiya, akwai wanda su ke quqqulla shi ga qasar harami guda biyu (ta Saudia), qarqashin tsare-tsare na qarya, da launukan tsegumi masu munanan manufa, wanda ake qulla makircinsu ga qasar da ta ke rayuwa akan addinin musulunci, a matsayin manhaja ko tsarin rayuwa, Qur'ani kuma da Sunnah a matsayin konsutushin.
Qasar da aikinta da ya fi muhimmanci shi ne hidimar harami biyu, wanda su ka qunshi matattarar imani (wato, Madina), da kuma wurin bege ko makomar zukatan Musulmai (wato, Makkah),
KU SAURARA!
Lallai wajibi ne akan kowane musulmi, alhalin yana sane da cewa, lallai wannan qasar, qasar kowani musulmi ne, kuma wurin begen kowani mumini, wajibi ne a kansa, ya samu yaqinin cewa, lallai yin gaba da wannan qasar, gaba ne da ma'abutan musulunci gaba xayansu, kuma tava tsaronta da zaman lafiyarta cutarwarsa da hatsarinsa zai tava kowane musulmi.
YA KU TARON MUSULMAI!...
Al'ummar musulmai tana rayuwa cikin xinbin canje-canje, da tashin-tashina, da abubuwa masu rikitarwa, da mushkiloli da tsanani da qunci.
Kuma lallai qasar harami biyu, ita ce cibiyar da ta fi girma, kuma tushen qasashen musulmai, kuma tava wannan qasar da sharri, lallai mafari ne na yin kaca-kaca ko kekketa, wannan al'ummar, kuma shi ne gudumar rusau da zai rushe haxin kan al'ummar, da wargajewar samuwarta, kuma saboda wannan qasar, ita ce ke bada kulawa ga harami biyu, da lamarin hajji da umrah, don haka ita ce alamar buwaya da xaukaka ga musulmai gaba xaya.
Kuma don haka ne, ya zama wajibi a kula da waxannan ma'anonin, a kuma haxa hannu don taimakon wannan qasar wajen aikata abinda a cikinsa alkhairin musulmai ya ke, da kuma kawo gyara ga halin da su ke ciki, Allah (تعالى) yana cewa: "Kuma ku yi taimakakkeniya, akan biyayya da taqawa, kuma kada ku yi taimakakkeniya akan zunubi da zalunci" [Ma'idah: 2].

YA KU BAYIN ALLAH…
Kuma lallai abinda ya xoru na wajibi, akan mutanen wannan qasar, ya fi girma, kuma alhakin da ya rataya a wuyansu lallai ya fi, wajen zama tamtar tsoka xaya, ko haxewa tare da jagororinsu, irin haxewar da soyayya za ta riqa bayyana da ita, da kuma girmamawa da jin umarninsu da yi musu biyayya, cikin abinda ba savon Allah ba, da taimaka wa juna wajen samar da abinda a cikinsa yardar Allah Mabuwayi da xaukaka ta ke, da kuma dukkan ababen da akwai maslaha da amfanin kowa-da-kowa, kuma yin hakan lalura ne da ta zama dole a shari'a, kuma maslahar qasa ce, kuma buqata ce ga dukkan mutane.
Kuma wajibi ne, a kiyaye bin kowace fitina, ko hanyoyi, ko kiraye-kirayen da su ke barazana ga qasarmu, ko za su iya shafar amincinta da zaman lafiyarta, kuma farillar da ta zama wajibi a shari'a ita ce, tsayuwar dako (daga kowani mutum), a matsayin sojoji, da su ke a haxe, su ke taimakakkeniya, don tunkuxe kowani mai jiran ganin sharri, da wanda zai kawo hari, ko ya yi ta'addanci, Allah (تعالى) yana cewa: "Kuma ku yi riqo da igiyar Allah gaba xaya, kada ku rarraba" [Ali-imrana: 103].
Kuma Allah (تعالى) ya ce: "Ya ku waxanda su ka yi imani ku yi xa'a wa Allah, kuma ku yi xa'a ga Manzonsa, da majivinta lamura daga cikinku" [Nisa'i: 59].

YA KU TARON MUSULMAI!...
Lallai mafi girman makami domin yaqar mushkilolin wannan al'ummar, da abinda ta ke fiskanta na qalu-balen da su ke fiskantarta (a koda-yaushe), da xinbin hatsarin da su ke kewaye da ita, shi ne YIN AIKI NA GASKIYA, DA XAUKACIN KARANTARWAR MUSULUNCI, a matsayinsa na salo kammalalle da ya game dukkan sha'anonin rayuwa. Tare kuma da yin aikin cikin da'irar 'YAN'UWANTAKA TA MUSULUNCI, DA GAMAYYA TA IMANI, "Lallai ne Mutum yana cikin hasara * sai dai waxanda su ka yi imani, kuma su ka yi aiki nagari, kuma su ka yi wasici da gaskiya, kuma su ka yi wasici da haquri" [Asr: 2-3].

'YA'UWANA MUSULMAI!...
Yana daga ni'imomimanya, ga wannan qasa (ta Saudia), DAIDAITUWAN LAMARI SHUGABANCI DA JAGORANCI, Wanda da su maslahohi na xaukacin al'umma da na xaixaikunsu gaba xaya su ke tsaruwa, kuma gamammun lomura da kevantattunsu su ke iya daidaituwa, kamar yadda Aljuwainiy ya ke faxa.

Kuma yana daga cikin haka, Abinda ya kasance a cikin waxannan dararen na zavin da ya yi daidai, wanda Sarki mai hidimar harami biyu maxaukaka ya yi; (wato, na zaven Yarimansa mai jiran gado, a cikin wani yanayi da ya cika da sanya albarka, daga kowa-da-kowa, Don haka; godiya ta qara tabbata ga Allah, akan abinda ya cika mana na ni'imar haxuwar zukata da rashin rarrabansu.
Kuma lallai Mu, a lokacin da mu ke mubaya'a ga Yarima mai jiran gado, akan littafin Allah, da sunnar ManzonSa, da kuma ji da biyayya, a cikin nashaxi ko tilasci, ko matsatsi ko sauqi, lallai muna roqon Allah, da ya sanya albarka cikin ayyukan sarki mai hidimar harami guda biyu, kuma ya tsawaita rayuwarsa cikin xa'ar Allah. Ya kuma datar da Yarima mai jiran karagar mulki, ya taimake shi kan ayyukansa, cikin abinda zai yardar da Allah (سبحانه), kuma ya sanya shi, ya zamo mabuxin alherori, marfin toshe kowane sharri, kuma ya sanya albarka cikin ayyukansa, kuma ya dabaibaye su da cin nasara da dace.

Allah ya kiyaye wannan qasar, da sauran qasashen musulmai, kuma ya datar da su gaba xayansu, zuwa ga ababen da yardarsa ta ke cikinsu.

ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, LA ILAHA ILLAL LAHU, WALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, WA LILLAHIL HAMD
            Allah yayi mini albarka NI da KU, cikin alqur'ani mai girma, ya kuma amfanar da NI da KU da abinda ke cikinsa na ayoyi, da tunatarwa mai hikima,      Ina faxar maganata wannan, kuma ina neman gafarar Allah, ku nemi gafararSa,    lallai shi Mai gafara ne Mai rahama.

HUXUBA TA BIYU
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, LA ILAHA ILLAL LAHU, WALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, WA LILLAHIL HAMD

YA KU 'YAN'UWANA MUSULMAI…
Ku daidaitu akan ayyukan biyayya ga Ubangijinku, kuma ku yi gaggawar neman samun yardarsa, a dukkan lokutanku, Allah (تعالى) yana cewa: "Kuma ka bauta wa Ubangijnka, har mutuwa ta zo maka" [Hijr: 99].

'YAN'UWANA MUSULMAI…
Wasiqar aminci ne da soyayya da gaisuwar idi za mu tura, ga zaratan sojojinmu, waxanda su ka xauki nauyin kare iyakoki, muna muku gaisuwar wannan idin,
Allah kuma ya girmama ladanku, ya ninninka sakayyarku,
Kuma ya kiyaye ku ta gaba gare ku, da ta bayanku,
Kuma Allah ya karvi waxanda su ka yi mutuwar shahada daga cikinku,
Ya kuma bada lafiya ga marasa lafiyan cikinku,
Ya warkar da waxanda aka musu rauni daga cikinku
Kuma ya qarfafi zukatanku, ya tabbatar da duga-duganku.

YA KU TARON MUSULMAI…
Musulunci addinin zaman lafiya ne da dukkan ma'anoninsa, da kuma haxin-kai da dukkan kalolinsa, da jin qai da tausayi da dukkan shakalolinsa, da kyautatawa da fiskokinsa masu yawa, sai ku bayyanar da hakan cikin ayyukanku, ku fito da shi a sarari a cikin mu'amalolinku, ku yaxa shi ga duniya, kamar yadda jerin halayyar Alqur'ani da kuma Annabi su ke, wajen tabbatar da dukkan aiki managarci, da kuma magana mai kyau.

Kuma hanyoyin qetare iyaka, da tsanantawa, da bin hanyoyin wuce gona-da-iri da ta'addanci, dukkan waxannan addinin musulunci ya yi hani akansu, kuma waxannan halayen ba su tsayawa a madadin karantarwar musulunci da manufofinsa da abinda musuluncin ke qoqarin cimmawa, "Kuma bamu turo ka ba, face jin-qai ga talikai" [Anbiya'i: 107].
"Kuma kada ku yi ta'addanci, saboda Allah baya son masu ta'addanci" [Baqara: 190].

Kuma lallai, Muna Allawadan kaiwan harin tsoratarwa, wanda ya auku kusa da xakin Allah mai alfarma, kuma wannan lamari ne mai girman muni, wanda addini da hankali basu amincewa da shi.
Kuma lallai Muna tsawatar da samarinmu, kan ruxuwa da irin wannan aikin, ko bin shexanun da su ke nufin ruguza addinin samarin, ko halaka su.
,,,          ,,,          ,,,

,,,          ,,,          ,,,

2017/06/16

21 ramadan 1438 hudubar juma'a daidai da 16 june 2017 DR. ABDULMUHSIN ALKASIM










HUXUBAR MASALLACIN ANNABI
 (صلى الله عليه وسلم)
JUMA'A, 21/RAMADHANA/1438H
Daidai da 15 /YULI / 2017M




LIMAMI MAI HUXUBA
DR. ABDULMUHSIN XAN MUHAMMADU XAN ABDURRAHMAN ALQASIM







TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
بسم الله الرحمن الرحيم
HUXUBAR FARKO
Lallai yabo na Allah ne; muna gode maSa, muna neman taimakonSa, muna neman gafararSa, kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kayukanmu, da munanan aiyukanmu.
Wanda Allah ya shiryar, babu mai vatar da shi, Wanda kuma ya vatar, to babu mai shiryar da shi.
Kuma ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; shi kaxai ya ke, bashi da abokin tarayya.
Ina kuma shaidawa lallai annabi Muhammadu bawanSa ne manzonSa ne.
Salatin Allah su qara tabbata a gare shi, da IyalanSa da SahabbanSa; da sallamar amintarwa mai yawa.

       Bayan haka;
Ku kiyaye dokokin Allah da taqawa -Ya ku bayin Allah- iyakar kiyayewa, kuma ku kiyaye shi, a asirce, da kuma a bayyane (a lokacin ganawa).

       Ya ku musulmai …
            Ubangijinmu (S.W.T) Mai karmici ne, Mai baiwa, TaskokinSa suna cike, Mulkin komai kuma, a hannunSa ya ke,
Ya zuba ni'imominSa ga bayinSa, kuma ya biyar da kyauta da falaloli, xaya bayan xaya a kansu,
Babu mai hana abinda ya bayar, kamar yadda babu mai bayar da abinda ya hana,
Kyautukan Allah basu da iyaka ta fiskar yalwa da yawa,
Yana yin kyautar alkhairori da karamomi,
Kuma kyautarSa tana ci-gaba bata yankewa, ta kuma game dukkanin halittunSa; sai alkhairorinSa su ka dawwama, falalolinSa da ni'imominSa su ka riqa saduwa,
Yana farar bayi da kyautar ni'imomi gabanin su roqe shi, kuma yana musu baiwar fiye da abinda ke xarsuwa a tunaninsu,
Babu wani a cikin sama da qasa, wanda baya cikin baiwar Allah,
Don haka, Allah shi ne wanda ya fi cancantar samun yabo da zikiri ko ambato akan ni'imominSa, ta hanyar tsantsanta soyayya, da bauta a gare shi, da kuma jingina ni'imomin zuwa gare shi, da yin amfani da ni'imomin cikin xa'a a gare shi.

Yana daga cikin BAIWOWINSA MAXAUKAKI afuwarSa ga wanda ya nufa daga cikin bayinSa, Allah (ta'alah) yana cewa: "Lallai ne Allah Mai afuwa ne, Mai gafara" [Haj: 60].
            Kuma Allah bai gushe ba yana afuwa ga zunuban bayinSa, ta hanyar barin yin uquba, ga dayawa daga cikinsu, matuqar basu masa shirka, ko su ka sanya masa kishiyoyi ba, Allah (ta'alah) yana cewa: "Kuma shi ne, wanda ke karvar tuban bayinSa, ya ke afuwa akan munana, kuma ya ke sane da abinda ku ke aikatawa" [Shura: 25].
            Mai afuwa ne, yana son afuwa, kuma yana son halittunSa su riqa aiki tuquru, domin samar da sabbuban afuwarSa, ta hanyar istigfari, da tuba, da imani, da ayyuka nagari.

            A cikin watan ramadhana kyautukan Allah da afuwarSa suna qara bayyana, watan falaloli da gafara, wanda a cikinsa ake ninninka ayyuka, ake kankare kura-kurai da zunubai, kuma a cikinsa ake bubbuxe qofofin rahama da aljannoni, ake sanya shexanu cikin qullin sarka, ake rurrufe qofofin wuta, watan azumi da karatun alqur'ani, da biyayya da kyautatawa, kasuwanci a cikinsa tare da Allah, ana ninninka shi, Ibnul-Jauziyرحمه الله- ya ce: "Ladan aiki yana qaruwa, saboda darajar lokaci, kamar yadda ke qaruwa idan aka halarto da zuciya, ko aka tsantsance niyya".

            Sallar dare, ita ce mafificin nafiloli bayan sallolin farilla, kuma Allah ya yi yabo ga bayinSa masu taqawa a cikin faxinSa: "Sun kasance a lokaci kaxan na dare su ke yin barci" [Zariyaat: 17].
            Kuma ya zo cikin hadisi cewa: "Wanda ya yi tsayuwar ramadhana (wato, sallar dararen watan) cikin imani da neman lada, to an gafarta masa abinda ya gabata daga zunubansa", Bukhariy da Muslim.
Kuma "Duk wanda ya yi sallolin dare tare da liman, har ya idar, to an rubuta masa ladan tsayuwan daren", Tirmiziy ya rawaito shi.
            Kuma duk wanda ya lazimci sallolin dare to ya cancanci shiga aljanna cikin aminci, Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa: "Ya ku mutane! Ku riqa yaxa sallama, ku ciyar da abinci, kuma ku sadar da zumunci, ku riqa sallah cikin dare, a lokacin da mutane ke barci, sai ku shiga aljanna da salama", Ahmad ya rawaito shi.

            Ita kuma SADAKA hujja ce kan imanin ma'abucinta, kuma kowani mutum yana qarqashin inuwar sadakarsa, a yinin qiyama, kuma mai ciyarwa an masa alqawarin samun xaukaka da gafara, Allah (سبحانه) yana cewa: "Kuma duk abinda kuka ciyar na kayan ciyarwa, ko, wani bakancen da ku ka yi, to lallai Allah yana saninsa" [Baqara: 270].
            Kuma ladan sadaka yana qara girma, idan aka gudanar da ita, a kwanaki masu falala. Kuma Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya kasance "shi ne, ya fi mutane kyauta, sai dai ya fi yawaita kyautar a cikin watan ramadhana", Bukhariy da Muslim.
            Kuma "yin UMRAH a watan azumi yana daidai da yin hajji", Bukhariy da Muslim.
            ADDU'A abu ne mai riba, wanda bashi da wata wahala, kuma addu'a shi ne bauta, kuma shi ne qashin bayan bauta, kuma da addu'a ake janyo wadaci, ake tunkuxe bala'oi, kuma mai azumi idan ya yi addu'a ba a mayarwa, Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa: "Mutane uku ba a mayar da addu'arsu; Mai azumi har zuwa lokacin buxa-baki, da shugaba adali, da addu'an wanda aka zalunta; Allah yana xaga ta saman girgije, kuma yana buxe mata qofofin sama, kuma Ubangiji yana cewa: Na rantse da buwayata! Zan taimake ki, koda bayan wani lokaci ne", Tirmiziy ya rawaito shi.

            ALQUR'ANI hujja ne, mai ceto, kuma shiriya da waraka, ma'abutansa; masu aiki da shi, su ne zavavvun halittu, kuma mafiya alheri, kuma su ne mutanen Allah, waxanda ya kevance, Allah ya yi musu alkawarin samun sakamako, da kuma qari daga falalarSa, a inda yake cewa: "Lallai waxanda ke karatun littafin Allah, kuma su ka tsayar da salla, kuma su ka ciyar daga abinda muka azurta su da shi, a asirce da a bayyane, to lallai suna fatan fatauci wanda bata tasgaro * domin Allah ya cika musu sakamakonsu, kuma ya musu qari daga falalarSa, Lallai shi Mai gafara ne Abin godiya" [Faxir: 29-30].

            LOKUTAN RAMADHANA fili ne mai faxi ga masu tsere a cikinsa, ayyukan biyayya da sadar da zumunci suna yawaita a cikinsa, kuma rayuka suna tsaftatuwa, halaye kuma suna tsarkaka, Halittu a tsakanin junansu suna kusantar juna, kuma sashinsu yana tausaya wa sashe.
            Lokaci ne mai albarka wanda musulmai su ke zage damtse a cikinsa, kuma ake xaga darajoji a cikinsa,
            Sai dai kash, ga kwanakin watan na ku (na ramadahana), suna shelanta, qarewa, kuma mai hankali shi ne wanda ya ribaci gomansa (na qarshe), sai ya rayar da su, da ayyukan kusanci, da xa'oi, ya kuma canza munanan ayyuka da kyawawa, sai ya kiyaye yininsa, ya rayar da darensa, kuma ya sanya Annabi (صلى الله عليه وسلم) ya zama abin koyinsa, jagora, domin ya kasance, "yana qara qoqarin bauta a goman qarshe, irin qoqarin da baya yi a sauran dararen", Muslim ya rawaito shi.
Kuma "Idan waxannan goman su ka shigo, ya kasance yana raya dare, yana kuma tayar da iyalansa, sai kuma ya daxa qoqari, ya qara zage damtse", Bukhariy da Muslim.
            A cikin waxannan dararen masu albarka, mustahabbi ne yawaita zikirin Allah, da karatun alqur'ani, Ibnu-Rajabin –رحمه الله- yana cewa: "Amma, lokuta masu falala, kamar watan azumi, musamman a dararen da ake neman lailatul qadari a cikinsu, to lallai mustahabbi ne a yawaita karatun alqur'ani, domin ribatar wannan zamanin".

            Kuma ya dace, Musulmi a cikin waxannan kwanakin ya yi kwaxayin aiki da ADDU'AR DA TA FI AMFANI, kuma ta fi gamewa, A'isha –رضي الله عنها- ta ce: Ya Ma'aikin Allah, idan na yi dacen lailatul qadari, me zan riqa faxa a cikinta? Sai ya ce:  "Ki ce, ALLAHUMMA INNAKA AFUWWUN TUHIBBUL AFWA FA'AFU ANNI, Ma'ana: Ya Allah, lallai ne kai, mai afuwa ne, kana son afuwa, ka min afuwa". Ahmad ya rawaito shi.
            I'ITIKAFIN waxannan goman sunnah ce da ta zo a sharia'a, saboda Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya yi i'itikafinsu, sa'annan sai matansa su ka cigaba da i'itikafinsu,
Ibnu-shihabin –Allah yayi masa rahama- yace: "Mamakin lamarin musulmai, sun bar yin i'itikaafi, alhalin Annabi (صلى الله عليه وسلم) bai bar yinsa ba tun da ya shiga garin Madina, kowace shekara, a cikin kwanaki goma na qarshen ramadhana, har Allah ya karvi ransa".
            Kuma ya dace, Mai i'itikafi, ya tsayu domin yin bauta, ya kuma shagaltu da manufar shar'anta i'itikafin, wanda ta fi girma, yana mai nisantar yawaita hulxoxi, da magana, ko yawaita ci, da barci.
Kuma ba zai fita daga masallacin ba, sai ga buqatar da babu makawa daga gare ta, Ibnul-qayyim –رحمه الله- ya ce: "Kuma manufar i'itikafi da ruhinsa, shi ne killace zuciya ga Allah, da tattara ta, a gare shi, da kevantuwa da shi, da yanke ko barin shagaltuwa da halittu, da shagaltuwansa da Allah; shi kaxai (S.W.T), ta yadda ambaton Allah (zikirinsa) da qaunarsa, da fiskantarsa, za su zama a gurbin tunani-tunanin zuciyarsa, da ababen da su ke xarsuwa a gare shi".

            Kuma a cikin DARAREN NAN GOMA NE, Musulmai ke neman dacewa da lailatul qadari, Manzon Allah –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Ku nemi lailatul qadari a darare goman qarshe, na watan ramadhana", Bukhariy da Muslim.
            Kuma an fi fatan samunta, a cikin dararen mara daga cikinsu, Manzo Allah –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Ku kirdadi lailatul qadari a cikin mara ko wutirin darare goman qarshe, na watan ramadhana", Bukhariy ya rawaito shi.
            Kuma acikin darare bakwai na qarshe, an fi fatan samun nata, saboda Manzon Allah –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Ku neme ta -yana nufin: lailatul qadari- a cikin goman qarshe, idan xayanku ya yi rauni ko ya gaza, to kada a rinjaye shi akan darare bakwai masu wanzuwa –na qarshe-", Muslim ya rawaito.
            Shekhul Ismlami Ibnu-taimiyyah –رحمه الله- yana cewa: "Sai dai wuturin zai kasance ne, tare da kula da abinda ya gabata; sai a nemi daren ashirin da xaya (21), da daren ashirin da uku (23), da kuma daren ashirin da biyar (25), da daren ashirin da bakwai (27), da daren ashirin da tara (29), ko kuma ya kasance tare da lura da dararen da su ka rage (daga watan), kamar yadda Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya ce: (a neme ta), ga darare tara wanda za su rage, ko ga bakwai waxanda za su rage, ko ga biyar waxanda za su rage, ko ga uku waxanda za su rage. A kan wannan, idan watan ya kasance kwanaki talatin ne (30), sai hakan ya kasance a cikin kwanaki na shafa'i, Sai ashirin da biyu (22), ya kasance, shi ne darare taran da su ka rage, sai kuma daren ashirin da huxu (24) ya kasance shi bakwai da za su rage, kuma da haka Abu-Said –رضي الله عنه- ya fassara shi, a cikin hadisi ingantacce. Kuma haka Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya tsayu a lamarin wata. Idan kuma lamarin ya kasance kamar haka, to lallai ya dace, Mumini ya yi kirdadon dacewa da lailatul qadari a cikin darare goman qarshen gab xayansu".

Daren LAILATUL QASARI dare ne mai girma; ma'abucin matsayi da daraja, kuma Allah ya saukar da sura sukutum akansa domin girmama sha'anin daren, da muhimmantar da lamarinsa, da xaukaka sha'aninsa, a inda ya ce: "To, me ya sanar da kai abinda ake cewa: Lailatul qadari?" [Qadr: 2].
Allah ya sanya ta mai albarka, mai yawan alheri, sai ya ce: "Lallai mu ne muka sauqar da shi a cikin wani dare mai albarka" [Dukhan: 3].
Kuma yada daga albarkar wannan daren, sauqar alqur'ani a cikinsa, Allah ta'alah yana cewa: "Lallai mu ne muka sauqar da shi (Alqur'ani) a daren qaddara" [Qadr: 1].
            Kuma a cikin daren Mala'iku ke sauka zuwa ga duniya, "Mala'iku da Ruhi suna sauka a cikinsa, da izinin Ubangijinsu, da kowani lamari" [Qadr: 4].
Ibnu-kasir –رحمه الله- ya ce: "Saukar Mala'iku yana yawaita, a cikin wannan daren ne, sabodab yawan albarkarta, kuma Mala'iku suna sauka ne tare da saukar albarka, da rahama, kamar yadda su ke sauka a lokacin tilawar qur'ani, kuma su ke kewaye halqoqin zikiri, kuma su ke shumfuxa fuka-fukansu ga xalibin ilimi na gaskiya, domin girmama shi".
            Dare ne na salama da aminci da natsuwa, Allah -تعالى- yana cewa: "Salama ne wannan daren, har fitar alfijir" [Qadr: 5].
Wato, dare ne da ya kuvuta daga sharrori.
            Raya wannan daren da ibadodi riba ne mai girma, Allah -تعالى- ya ce: ''Lailatul qaradi ya fi yawan alkhairi fiye da watanni dubu" [Qadr: 3].
An-Nakha'iyرحمه الله- ya ce: "Yin aiki a cikin wannan daren, ya fi alkhairi akan yin aiki a cikin watanni dubu".
            Wanda ya rabauta da wannan daren, shi ne wanda ya tsayu a cikinta, yana mai gaskata alqawarin Allah, yana kuma neman lada, ba wata manufar ta daban ba; kamar riya, da makamancinta, Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Wanda ya yi tsayuwar lailatul qadari cikin imani da neman lada, to an gafarta masa abinda ya gabata daga zunubansa".
            Kuma a cikin wannan daren ake qaddara dukkan qaddarar da za ta samu halittu gaba xaya, na xaukacin shekara, sai ya a yanko shi daga jikin lauhul mahfuz, zuwa ga Mala'iku marubuta, sai abin da zai kasance ya bayyana musu, sai kuma Allah ya umarce su da aikata abinda aikinsu ne, kamar yadda Allah -تعالى- ya ke cewa: "A cikin daren, ake rarrabe kowani lamari da ake hukuntawa * Lamari ko umarni ne daga wajenmu, lallai mun kasance masu aikewa" [Dukhan: 4-5].

          BAYAN HAKA, YA KU MUSULMAI!
            Ayyuka ana lura da abinda aka gama su ne, kuma lallai abin luran shi ne kamalar qarshen ayyuka, ba tawayar farkonsu ba; don haka; duk mutumin da a farkon watansa ya kasance ya mayar da lamari ga Allah, aikinsa kuma ya yi dacen Sunnah, to sai ya qara kyautata gininsa, ya kuma yi godiya wa Allah, kan ni'imomi, kuma kada ya kasance kamar wadda ta warware zaren saqarta, bayan tukka ta yi qarfi, ya zama warwararru.
            Wanda kuma ya munana a cikin kwanakin da su ka shuxe, to sai ya tuba cikin abinda ya rage; saboda qofar tuba a buxe ta ke, kuma baiwar Allah abar bayarwa ce.
Kuma "Kuma wanda ya bi Allah da taqawa, Allah zai sanya masa mafita" [Xalaq: 2].

A UZU BILLAHI MINASH SHAIXANIR RAJIM:
"Yak u waxanda su ka yi imani, idan ku ka bi Allah da taqawa, zaisanya muku ma'aunin rarrabewa (na ilimi)" [Anfal: 29].

            ALLAH YAYI MINI ALBARKA NI DA KU CIKIN ALQUR'ANI MAI GIRMA. …
             



HUXUBA TA BIYU
Yabo ya tabbata ga Allah kan kyautatawarSa;  Godiya kuma tasa ce bisa ga datarwarSa da kuma ni'imominSa,
Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; shi kaxai ya ke bashi da abokin tarayya; Ina mai girmama sha'aninSa.
Ina kuma shaidawa lallai annabinmu Muhammadu bawansa ne, kuma manzonSa.
Ya Allah, ka yi daxin salati a gare shi, da iyalansa da sahabbansa, da kuma sallama mai ninnukuwa.

Ya ku musulmai…
            Duniya awowi ne da kwanaki, kuma tana da shekarun da aka xibar mata, shekarun mutum a cikinta kuma, sune wanda ya yi aiki a cikinsu.
Lallai Mai rabo, shi ne wanda ya dawwamar da ambaton duniya, da mafi kyan ayyuka, kamar yadda Wanda ya ci nasara  shi ne, ya ribaci daqiqoqin lokacinsa, kuma bai yi sakaci cikin wani abu na zamaninsa ba.
            Wanda ya faxi babu nauyi, kuma shi ne mutumin da lamuransa su ka sakwarkwace masa, zuciyarsa ta gafala, ya kuma bi son zuciyarsa.
Marashin rabo, shi ne wanda aka hana shi aikin alheri a cikin watan azumi, tavavve kuma shi ne wanda ya yi hasarar lakuta masu falala, Manzon Allah –صلى الله عليه وسلم- yana cewa: "Turvaya ta bugi hancin mutumin da, watan Ramadhana ya shigo, har ya fita, sai ba a gafarta masa ba",  Tirmiziy ya rawaito shi.
>>> 

            Sannan ku sani, lallai Allah ya umarce ku da yin salati da sallama ga annabinSa, a cikin mafi kyan littafinSa, inda ya ce: "Lallai ne Allah da Mala'ikunSa, suna yin salati ga wannan Annabin, Ya ku waxanda su ka imani, ku yi salati a gare shi, da sallamar amintarwa", [Ahzab: 56].

            Ya Allah! Ka yi salati da sallama da albarka, ga annabinmu Muhammadu,
            Kuma Ya Allah! Ka yarda da khalifofi shiryayyu, waxanda suka yi hukunci da gaskiya, kuma da shi, su ka kasance suke yin adalci, Abubakar da Umar da Usman da Aliyu, da kuma sauran sahabbai gabaxaya, Ka haxa da Mu tare da Su, da kyautarka da karamarka, Ya Mafi kyautar masu kyauta.
            Ya Allah! Ka xaukaka Musulunci da Musulmai, ka qasqantar da shirka da Mushirkai, kuma ka ruguza maqiyan addini, Kuma ka sanya –Ya Allah!- Wannan qasar cikin aminci da nitsuwa, da wadaci da walwala, da kuma sauran qasashen Musulmai.


                Bayin Allah!!!
                "Lallai Allah yana yin umurni da adalci, da kyautatawa, da baiwa makusanci, kuma yana yin hani akan alfasha da abin qi, da zalunci, Yana muku wa'azi da fatan zaku zama masu tunawa" [Nahli: 90].
Ku riqa ambaton Allah Mai girma da daraja zai ambace ku, ku gode masa akan ni'imominSa zai muku qari, kuma ambaton Allah shine mafi girma, kuma lallai Allah ya san abinda kuke aikatawa.


TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...