2018/06/27

HUDUBAR MASALLACIN ANNABI saw JUMA'A, 15 SHAWWAL 1439H ta Dr. Abdulmuhsin Alkasim











HUDUBAR MASALLACIN ANNABI
 (صلى الله عليه وسلم)
JUMA'A, 15/SHAWWAL/1439H
Daidai da 29 /YUNIYO / 2018M




LIMAMI MAI HUDUBA
DR. ABDULMUHSIN DAN MUHAMMADU DAN ABDURRAHMAN ALKASIM





TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
TSARKAKE RAYUKA DA KOKARIN GYARA SU
تزكية النفوس وإصلاحها
Shehin Malami wato: Abdulmuhsin bn Muhammadu bn Abdurrahman Alkasim –Allah ya kiyaye shi- ya yi hudubar juma'a mai taken: TSARKAKE RAYUKA DA KOKARIN GYARA SU, Wanda kuma a cikinta ya tattauna, akan abinda ke tafe, Ya ce:

بسم الله الرحمن الرحيم
HUDUBAR FARKO
Lallai yabo na Allah ne; muna gode maSa, muna neman taimakonSa, muna neman gafararSa, kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kayukanmu, da munanan ayyukanmu.
Wanda Allah ya shiryar, babu mai batar da shi, Wanda kuma ya batar, babu mai shiryar da shi.
Kuma ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; shi kadai ya ke, bashi da abokin tarayya.
Ina kuma shaidawa lallai annabi Muhammadu bawanSa ne manzonSa ne.
Salatin Allah su kara tabbata a gare shi, da IyalanSa da SahabbanSa; da sallamar amintarwa mai yawa.

        Bayan haka;
Ku kiyaye dokokin Allah da takawa -Ya ku bayin Allah- iyakar kiyayewa, kuma ku kiyaye shi, a asirce, da kuma a bayyane (a lokacin ganawa).

        Ya ku musulmai …
GYARUWAN HALITTU DA TSAYUWAR LAMURANSU, YANA CIKIN BAIWA HALITTU HAKKOKINSU, kuma wannan shine adalcin da Sammai da Kassai suka tsayu da shi, kuma akansa Duniya da Lahira suka tsayu.
Kuma kowace Rai, tana da wani hakki akan sahibinta, wanda za a tambaye ta akansa, a ranar sakamako, Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Kuma lallai Ranka tana da hakki akanka", Ahmad ya ruwaito shi.
Kuma mafi girma daga cikin hakkokin Rai, shine tsarkake ta.
Kuma da haka ake kiyaye ta daga lalacewa da hallaka, saboda Rayuka an dabi'antar da su akan halaye ababen zargi, wannan ya sanya suke yawaita umurni da mummuna, kamar yadda Allah Ta'alah ya ce: "Lallai ne Rai, hakika mai yawan umurni ne da mummunan aiki ne", [Yusuf: 53].
Kuma tana da sharri, wanda ake neman tsarin Allah daga gare shi, Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Ina neman tsarinka daga sharrin raina", Ahmad ya ruwaito shi.
Kuma Annabi –صلى الله عليه وسلم- yana fada a farkon hudubarsa, cewa: "Kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kayukanmu", Tirmiziy ya ruwaito shi.
Don haka, babu makawa dole sai an nemi gyaruwansu.
Kuma Allah yana son hakan ga bayinSa, Allah Ta'alah ya ce: "Allah baya nufin ya sanya wani kunci akanku, saidai yana nufin ya tsarkake ku –zahirinku da badininku-", [Ma'ida: 6].

Kuma SABODA GIRMAN LAMARIN TSARKAKE RAYUKA, SAI HAKAN YA ZAMA DAYA DAGA CIKIN MAFUFOFIN TURO MANZANNI,
Saboda ga annabi Ibrahim da Isma'ila –عليهما السلام- a lokacin da suka kasance suna rokon Allah, akan ya turo wani Manzo daga cikinsu domin ya tsarkake su, a inda suke cewa: "Kuma Ya Ubangijinmu! Ka aiko da wani manzo a cikinsu, yana karanta musu ayoyinka, kuma yana karanta musu littafi da hikima, kuma yana tsarkake su", [Bakara: 129].

Kuma annabi Musa, Allah ya tura shi zuwa ga Fir'auna sai ya ce masa: "Ka tafi zuwa ga Fir'auna lallai shi ya yi dagawa * sai ka ce: shin ko za ka so ka tsarkaka?", [Nazi'at: 17-18].

Kuma Allah ya turo Annabinmu Muhammadu –صلى الله عليه وسلم- domin ya tsarkake bayi, Allah Ta'alah ya ce: "Shine wanda ya aiko a cikin ummiyawa (marasa rubutu da karatu) wani Manzo daga cikinsu, yana karanta musu ayoyinSa, kuma yana tsarkake su, kuma yana koyar da su littafi da hikima", [Jumu'ah: 2].
Kuma da hakan Allah ya yi babbar falala ga bayinSa muminai, a inda ya ce: "Kuma hakika, Allah ya yi babbar baiwa ga muminai, yayin da a cikinsu ya aika Manzo daga ainihinsu, yana karanta ayoyinSa a gare su, kuma yana tsarkake su, kuma yana karantar da su littafi da hikima", [Ali-imrana: 164].

Mai yin da'awa zuwa ga Allah ba zai kawar da fiskarsa ga wani mutum ba, koda kuwa bashi da wani matsayi, saboda kwadayin tsarkakarsu da shiriyarsu, Allah ya ce: "Ya daure fiska kuma ya juya baya * saboda makaho ya je masa * to me ya sanar da kai, la'alla watakila shine zai tsarkaka", [Abasa: 1-3].
Kuma samun rabo gaba dayansa, lallai yana cikin tsarkake Rai,
Tabewa kuma da yin hasara suna cikin kishiyan haka, kuma akan wannan ne Allah Ta'alah ya yi rantsuwa da mafi tsawon rantsuwa a cikin littafinSa, sa'annan ya ce: "Lallai ne wanda ya tsarkake Rai ya samu babban rabo * Wanda kuma ya turbude ta da laifi, ya tabe", [Laili: 9-10].
Katadah da waninsa suka ce: "Lallai ya samu babban rabo, wanda ya tsarkake Ransa da 'da'a ga Allah, da kuma ayyuka nagari".

Kuma wannan shine manzanci gaba daya suka hadu akansa, Allah Ta'alah ya ce: "Lallai ne wanda ya tsarkaka (da imani) ya samu babban rabo * kuma ya ambaci sunan UbangijinSa, sa'annan ya yi sallah * kuma lallai kuna zabin rayuwa ta kusa (Duniya) * alhali Lahira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa *  lallai wannan yana cikin littafan farko * wato, littafan Ibrahima da Musa" [A'alah: 14-19].

Kuma yana daga sifofin Muminai, tsarkake rayukansu, Allah Ta'alah ya ce: "Sune wadanda, ga tsarkaka masu aikatawa ne", [Muminuna: 4].
Ibnu-kasir –رحمه الله- ya ce: "shine zakkar tsarkake rayuka, da kuma zakkar dukiya, kuma Mumini kamili, shine wanda yake aiki da wannan, kuma yake aiki da wancan".

Kuma duk wanda Ransa ta tsarkaka, to hakika Allah ya masa babban baiwa, kuma ya karrama shi, Allah Ta'alah ya ce: "Ba domin falalar Allah akanku ba, da rahamarSa, babu wani Mutum daga cikinku da zai tsarkaka har abada" [Nur: 21].

Kuma Aljannah a Lahira, sakamako ne na Wanda ya gyara kansa, Allah Ta'alah ya ce: "kuma amma wanda ya ji tsoron tsayuwa a gaba ga UbangijinSa, kuma ya kange kansa daga son rai * to lallai Aljannah ita ce makoma", [Nazi'at: 40-41].

Kuma darajoji madaukaka a cikin Aljannah shine sakamakon wanda ya tsarkake ransa, Allah Ta'alah ya ce: "Kuma wanda ya je masa yana mai imani, alhali ya aikata aikin kwarai, to lallai wadannan suna da darajoji madaukaka * a gidajen Aljannar zama, koguna suna gudana daga karkashinsu, suna masu dawwama a cikinsu, kuma wannan shine sakamakon wanda ya tsarkaku", [Daha: 75-76].

Kuma yin aiki domin tabbatar da wannan baiwar wajibi ne, akan dukkan bayi, wannan kuma ta hanyar aiki da umurnin Allah, da nisantar haninsa, domin babbar manufa cikin umurni da hani –bayan tabbatar da bauta ga Allah- shine tsarkake rayuka da gyaran su.
Kuma lallai yana daga manyan manufofi, a cikin shari'a: Kiyaye rayuka, kuma kaiwa makura wajen kiyaye su, shine aiki domin tsarkake su.

Kuma mafi girman ababen da rayuka suke tsarkaka da su, shine TAUHIDIN ALLAH, ta hanyar yin bauta a gare shi; shi kadai, bashi da abokin tarayya, kuma lallai babu wani tsarkaka ga rayuka, sai ta hanyar tauhidi, Allah Ta'alah ya ce: "Kuma bone ya tabbata ga masu yin shirka * wadanda basu zowa tsarkaka, kuma su a game da Lahira su kafirai ne", [Fussilat: 6-7].
Shekhul-Islam IbnuTaimiyyah –رحمه الله- ya ce: "shine tauhidi da imani, wanda rai ke tsarkaka da su, saboda yana kunsar kore bauta ga wanda ba Allah ba, daga cikin zuciya, da tabbatar da cancantar bauta ga Allah daga cikin zuciya, wanda shine hakikanin LA ILAHA ILLAL LAHU, kuma wannan shine ginshiki na ababen da suke tsarkake Rai".

        Kuma SALLAH tsarki ne ga Rai, kuma tsarkaka ga Bawa, Allah Ta'alah ya ce: "Lallai ne sallah tana hana alfasha da munkari", [Ankabut: 45].
Kuma tana gyara ma'abutanta; sai ta tafiyar musu da kura-kurai, Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Ku bani labari, da za a samu wani kogi a kofar dayanku, sai yake yin wanka a cikinsa kullum sau biyar, shin wani abu na dattinsa zai wanzu? Sai suka ce, a'a! babu wani abu na dattinsa da zai saura, sai ya ce: to wannan shine misalin salloli guda biyar; Allah yana share kura-kurai da su", Bukhariy da Muslim.

Kuma da ZAKKAH rayuka suke tatuwa kuma suke tsarkaka, Allah Ta'alah ya ce: "Ka karbi sadaka daga dukiyarsu, kana mai tsarkake su, kuma kana mai tabbatar da kirkinsu da ita", [Tauba: 103].
Kuma tsira daga fadawa Wuta shine sakamakon wanda ya tsarkake Ransa, Allah S.W.T ya ce: "Kuma da sannu za a nisantar da mafi takawa daga fadawa cikinta * wanda yake bayar da dukiyarsa, yana neman tsarkaka", [Laili: 17-18].

Kuma AZUMI kariya ne daga cutukan rayuka da sharrace-sharracensu, kuma fidiya ga ma'abutansa daga ayyukan alfasha, Allah Ta'alah ya ce: "Ya ku wadanda suka yi imani an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabta shi ga wadanda suke gabaninku, la'alla zaku samu takawa", [Bakara: 183].

Kuma a lokacin HAJJI rayuka suna tsarkaka, Allah Ta'alah ya ce: "Kuma wanda ya yi niyyar hajji a cikinsu, to babu kwarkwasa, kuma babu fasikci, kuma babu jayayya a cikin hajji", [Bakara: 197].
        Kuma wanda ya samu karbuwa daga cikin Mahajjata zai koma yana tsarkakakken Rai, kamar ranar da Mahaifiyarsa ta haife shi, Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "wanda ya yi hajji domin Allah, bai yi kwarkwasa ba, kuma bai yi fasikci ba, zai koma kamar ranar da Mahaifiyarsa ta haife shi", Bukhariy da Muslim.

        Kuma ADDU'A ibada ce mai girma, kuma da ita ce, bawa ke samun abin nemansa, kuma Allah S.W.T  a hannunSa gyaruwan zukata suke da tsarkinsu, Allah Ta'alah ya ce: "Kawai Allah ne ke tsarkake wanda ya ga dama", [Nisa'i: 49].
Kuma daga cikin addu'oin Annabi –صلى الله عليه وسلم- fadinsa "Ya Allah! Ka baiwa raina takawarta, ka tsarkake ta, domin kai ne mafi alherin wanda zai tsarkake ta", Muslim.

        Kuma yawaita AMBATON ALLAH cikinsa akwai yalwatar zuciya, da tsarkin Rai, Allah Ta'alah ya ce: "Lallai da ambaton Allah zukata suke natsuwa", [Ra'ad: 28].

Kuma duk wanda ya shagaltu da ALKUR'ANI yana tilawarsa, yana tadabburin ma'anoninsa, yana aiki da shi, yana koyansa yana koyar da shi, sai Ransa ta gyaru, kuma ta mika wuya zuwa ga Allah, Allah Ta'alah ya ce: "Ya ku Mutane! Hakika wa'azi ya zo muku daga Ubangijinku, da warakar abinda ke cikin kiraza, da shiriya da rahama ga Muminai", [Yunus: 57].
Ibnul-kayyim –رحمه الله- ya ce: "Alkur'ani shine magani cikakke, daga dukkan cutukan zuciya da jiki, da cutukan Duniya da Lahira".

Kuma ILIMI mai amfani yana tsarkake ma'abutansa, kuma shi ilimin shine ke nuna musu hanyar samun tsarkakan Rai, Allah Ta'alah ya ce: "Shin, wanda yake mai tawali'u sa'oin dare, yana mai sujada, kuma yana mai tsayuwa ga sallah, yana tsoron Lahira, kuma yana fatan rahamar UbangijinSa, (wannan yana zama daidai da waninsa?), Ka ce: shin wadanda suka sani suna daidaita da wadanda ba su sani ba? Kawai wadanda suke tunani sune masu hankali!", [Zumar: 9].
Kuma ilimi ba zai gushe yana tare da ma'abucinsa ba, har sai ya kai kololuwar tsarkaka, sai ya kasance daga ma'abuta ibadar tsoron Allah, Allah Ta'alah ya ce: "Kawai Malamai ne ke tsoron Allah, daga cikin bayinSa", [Fadir: 28].

Kuma KARANTA TARIHIN Maluma da gwaraza yana zaburar da Rayuka, su yi koyi da su, da kokarin shiga tawagarsu, kuma duk wanda ya yi nazari cikin tarihin magabatanmu, sai sakacinsa ya bayyana a gare shi.

Kuma da gyaruwar zuciya ne, da tsarkakarta gyaruwan zahirin bawa da badininsa suke, kuma duk wanda ya yi gwagwarmaya da Ransa, to sai ya rabauta da samun makasudinsa.
Kuma dawwamar da KIYAYAR ALLAH, yana mayar da ma'abutansa kamilai, sai su riski matakan bayi masu kyautata ibada.

Kuma tsarkakar Rai, yana rataya ne akan yin hisabi a gare ta, saboda Rai bata tsarkakuwa kuma bata gyaruwa sai idan ana mata hisabi, kuma da aikata hakan bawa zai iya tsinkayar aibobin Ransa, sai kuma ya yi aiki tukuru wajen gyara su.

Kuma RUNTSE IDANU yana daga abinda Rai ke tsarkaka da shi, Allah Ta'alah ya ce: "Ka ce wa Mumianai su rika runtse sashen ganinsu, kuma su kiyaye farjojinsu, Wannan shine mafi tsarki a gare su", [Nur: 30].
Kuma Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Ya ku taron samari! Wanda ya samu iko daga cikinku ya yi aure, domin aure yafi runtse idanu, kuma yafi katange farji, Wanda kuma bai samu ba, sai ya yi azumi, domin shi a wurinsa kamar fidiya ne", Bukhariy da Muslimsuka ruwaito shi.
        Kuma katange Rai daga yawaita kalle-kalle da yawar magana yana daga sabbuban tsarkinta, Ibnul-kayyim –رحمه الله- ya ce: "kuma mafi yawan sabo, lallai suna haifuwa ne daga yawar magana da yawaita kalle-kalle, kuma sune kofofin da suka fi fadi daga cikin kofofin da Shedan ke shigowa, saboda wadannan gabban ba su cika kosawa ba".

Kuma "Aboki yana kan addinin abokinsa ne, sai dayanku ya yi dubi, cewa da wa yake abota", kuma lallai samun abota ta gari taimako ne mafi alheri kan isa ga lamura madaukaka, saboda idan ya gafala, sai abokansa su tuna masa, idan kuma ya tuna sai su taimake shi.

Kuma cikin ZIYARTAR MAKABARTA, da TUNA MUTUWA, rayuwar zukata da daidaituwarsu suke.

Ita kuma TUBA tana tsarkake bawa, kuma tana wanke shi, Allah Ta'alah ya ce: "Kuma ku tuba zuwa ga Allah, ya ku Muminai, tsammanin ku samu babban rabo", [Nur: 31].
"Kuma lallai bawa idan ya aikata laifi, sai a diga masa wani digo baki a jikin zuciyarsa, idan kuma ya bar laifin, ya nemi gafara, ya tuba, sai a kankare masa shi", Tirmiziy ya ruwaito shi.
Shekhul Islam Ibnu-taimiyyah –رحمه الله- ya ce: "Rai da ayyuka, ba su tsarkaka, sai an gusar musu da abinda ke warware alheri daga jikinsu, kuma Mutum ba zai kasance mai tsarkaka ba, face ya bar sharri, don haka, TAZKIYYAH, duk da cewa asalinsa shine bunkasa, da albarka, da karuwar alkhairi, to lallai tana kasancewa ne, idan aka gusar da sharri, wannan ya sanya mai tsarkaka dole ya hada wannan, da kuma wannan".

        BAYAN HAKA, YA KU MUSULMAI!
        Asalin da ke bayanin yadda ake samun tsarkakar RAI shine littafin Allah, da sunnar Manzon Allah –صلى الله عليه وسلم-, ta hanyar yin biyayya ga Allah, da bin shiriyar Annabi –صلى الله عليه وسلم-.
Kuma wannan shine hanyar Allah, da addininSa, da kuma turbarSa mikakkiya.
Kuma da haka ake samun tsarkin Rayuka da gyaruwansu, da rabautar halittu da daukakansu.


A UZU BILLAHI MINASH SHAIDANIR RAJIM:
"Kuma wanda ya nemi tsarkaka, to lallai yana tsarkaka ne domin kansa", [Fadir: 18].

        ALLAH YAYI MINI ALBARKA NI DA KU CIKIN ALKUR'ANI MAI GIRMA. …
         

HUDUBA TA BIYU
Yabo ya tabbata ga Allah kan kyautatawarSa, kuma godiya tasa ce, akan datarwarSa da ni'imominSa,
Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya; ina mai girmama sha'aninSa,
Kuma ina shaidawa lallai annabinmu Muhammadu bawanSa ne, kuma manzonSa,
Ya Allah, ka yi dadin salati a gare shi, da iyalansa da sahabbansa, da sallamar amintarwa mai ninninkuwa

Ya ku Musulmai…
        Canzuwar halayen bayi; ta fiskar gyaruwansu da baci, da wadaci da tsanani, da aminci da tsoro, yana ratayuwa ne da canjuwan abinda ke cikin Rayukansu, Allah Ta'alah ya ce : "Lallai Allah baya canza abinda yake ga Mutane, sai sun canja abinda yake ga zukatansu", [Ra'ad: 11].
        Kuma duk abinda ke samun bayi tushensa daga kayukansu ne, Allah Ta'alah ya ce: "Shin, a lokacin da wata masifa ta same ku, alhali kuwa kun samar da biyunta, sai ku ke cewa: Daga ina wannan ya ke? ka ce: daga wurin kayukanku ne", [Ali-imrana: 165].
        Kuma duk wanda ya gyara zuciyarsa sai Allah ya gyara masa zahirinsa.
        Kuma duk wanda ya gyara tsakaninsa da tsakanin Allah, sai Allah ya gyara masa tsakaninsa da tsakanin Mutane.
        Kuma duk wanda ya yi aiki domin Lahirarsa, sai Allah ya isar masa a lamarin Duniyarsa.

        Mumini mai yawan tsoro ne a zuci, saboda yana hada tsakanin kyautata aiki da tsoro, sai yake kokarin gyara kansa da tsarkake Ransa, amma kuma baya neman a yabe shi da aikata hakan, Allah Ta'alah ya ce: "saboda haka, kada ku tsarkake kanku, shine mafi sani ga wanda ya yi takawa ", [Najm: 32].

>>> 
        Sannan ku sani, lallai Allah ya umarce ku da yin salati da sallama ga annabinSa, a cikin mafi kyan littafinSa, inda ya ce: "Lallai ne Allah da Mala'ikunSa, suna yin salati ga wannan Annabin, Ya ku waxanda su ka imani, ku yi salati a gare shi, da sallamar amintarwa", [Ahzab: 56].
        Ya Allah! Ka yi salati da sallama da albarka, ga annabinmu Muhammadu,
       

        Bayin Allah!!!
          "Lallai Allah yana yin umurni da adalci, da kyautatawa, da baiwa makusanci, kuma yana yin hani akan alfasha da abin qi, da zalunci, Yana muku wa'azi da fatan zaku zama masu tunawa" [Nahli: 90].
Ku riqa ambaton Allah Mai girma da daraja zai ambace ku, ku gode masa akan ni'imominSa zai muku qari, kuma ambaton Allah shine mafi girma, kuma lallai Allah ya san abinda kuke aikatawa.

2018/06/24

Masu warware Musulunci (النواقض العشرة)



  Masu warware Musulunci
(النواقض العشرة)
Bismillahir-Rahmanir-Rahim!

Ka sani! Lallai abubuwan da suke warware Musulunci goma ne:


1) Shirka cikin bautar Allah Madaukaki. Allah Ta'alah yana cewa:


“Lallai ne Allah ba ya gafarta ayi shirka da shi, kuma yana gafarta koma bayan haka, ga wanda yake so” (Nisa, 116.)

Kuma ya ce:
“Lallai, wanda ya yi shirka da Allah, to lallai Allah ya haramta masa Aljanna, kuma makomarsa Wuta ce, kuma azzalumai basu da masu taimakawa” (Ma'ida, 72.)
Daga cikin shirka akwai: Yin yanka ga wanda ba Allah ba, kamar mai yin yanka ga Aljani ko ga kabari.

2) Wanda ya riki tsani tsakaninsa da tsakanin Allah; yana rokonsu yana neman ceto daga gare su, yana dogaro akansu, ya kafirta, da ijma'i.

3) Wanda bai kafirta mushirkai ba, ko ya yi shakka kan kafircinsu, ko yake inganta addininsu da suke tafiya akai, ya kafirta.

4) Wanda ya kudurta cewa lallai shiriyar waninsa –sallal Lahu alaihi wa sallama- wai tafi ta Annabi kamala, ko kuma hukuncin wanin Annabi yafi kyau akan hukuncin Annabi, kamar wadanda suke fifita hukuncin 'Dagutai akan hukuncinsa, to wannan kafiri ne.

5) Wanda ya kyamaci wani abu, daga cikin abubuwan da Manzon Allah –sallal Lahu alaihi wa sallama- ya zo da su, koda ya yi aiki da shi, to ya kafirta.

6) Wanda ya yi izgili  da wani abu na addinin Manzon Allah, ko ladan Allah, ko ukubarsa, ya kafirta, Dalili kuma shine fadinsa Madaukaki:
“Ka ce: Shin da Allah da kuma ayoyinsa da Manzonsa kuka kasance kuke izgili * kada ku kawo wani uzuri, hakika kun kafirta bayan imaninku'” (Tauba, 65-66)

7) Sihiri. Daga cikinsa akwai: sihirin juya masoya, dana kulla su, Duk wanda ya aikata shi, ko ya yarda da shi, ya kafirta, Dalili akan haka shine fadinsa Madaukaki:


“Kuma basu ilmantar da wani Mutum, face sun ce: Mu jarrabawa ce kawai, saboda haka kada ka kafirta” (Bakara, 102).


8) Agazawa Mushirkai da basu taimako akan Musulmai. Dalili akansa shine fadinsa Madaukaki:


“Wanda ya jibince su daga gare ku, to, lallai ne shi yana daga gare su, Lallai Allah ba ya shiryar da Mutane azzalumai” (Ma'ida, 51).


9) Wanda ya kudurta cewa, lallai wasu Mutane ya halatta musu su fice daga shari'ar annabi Muhammadu –sallal Lahu alaihi wa sallama-. Kamar yadda bawan Allah Khadir ya fita daga tsarin shari'ar annabi Musa –sallal Lahu alaihi wa sallama-, to shi mai wannan kudurin ya kafirta.

10) Bijire wa addinin Allah Ta'alah. Ta yadda zai kasance baya koyansa kuma baya aiki da shi, Dalili kuma shine fadinsa Madaukaki:


“Babu wanda yafi zalunci, bisa ga wanda aka tunatar da ayoyin Ubangijinsa, sa'annan ya bijire daga barinsu, Lallai Mu masu yin azabar ramuwa ne ga masu laifi” (Sajada, 22)


Ba banbanci cikin wadannan ababe masu warware Musulunci, tsakanin mai wargi da mai yi da gaske, da wanda yake tsorace, saidai wanda aka tilasta. Kuma dukkansu suna da girman hatsari, kuma suna yawaita aukuwa; don haka ya dace Musulmi ya kiyaye su, kuma ya ji tsoronsu ga kansa. Muna neman tsarin Allah daga ababen da suke hukunta fushinsa da ukubarsa mai radadi.


Allah ya yi dadin salati ga fiyayyen halittarsa; Muhammadu, da iyalansa da sahabbansa, da sallamar amintarwa.


2018/06/22

HUDUBAR MASALLACIN ANNABI 8 Shawwal 1439H daidai da 22Yuni2018M ta Dr. Bu'aijan












HUDUBAR MASALLACIN ANNABI
(صلى الله عليه وسلم)
JUMA'A, 08/Sawwal/1439H
daidai da 22/Yuni/ 2018M



LIMAMI MAI HUDUBA
SHEIKH ABDULLAHI BN ABDURRAHMAN ALBU'AIJAN





TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
BADA KULAWA KAN LOKATAI, DA RASHIN TOZARTA HAKKOKI DA WAJIBAI
Shehin Malami wato: Abdullahi bn Abdurrahman Albu'aijan –Allah ya kiyaye shi- ya yi hudubar juma'a mai taken: RIBATAR LOKACI, Wanda kuma a cikinta ya tattauna, akan abinda ke tafe, Ya ce:

بسم الله الرحمن الرحيم
HUDUBAR FARKO
Yabo ya tabbata ga Allah muna gode maSa, muna neman taimakonSa, kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kayukanmu da munanan ayyukanmu, Wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, wanda kuma ya batar, babu mai shiryar da shi.
Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah.
Kuma ina shaidawa lallai annabi Muhammadu bawanSa ne, manzonSa.
Allah yay i dadin salati a gare shi, da iyalansa da sahabbansa, da sallamar amintarwa mai yawa.

Ya ku bayin Allah…
Ina muku wasici da ni kaina, da bin dokokin Allah Mabuwayi da daukaka, domin ita ce wasiyyar Allah ga halittar farko dana karshe, "Kuma hakika mun yi wasiyya ga wadanda aka baiwa littafi a gabaninku, da ku, cewa ku bi Allah da takawa" [Nisa'i: 131].

Ya ku taron Musulmai…
Ku yi takawar Allah Ta'alah, kuma ku rigayi shekarunku da ayyukanku, kuma zantukanku su rika tabbatar da ayyukanku, domin hakikanin rayuwar Mutum shine abinda ya aiwatar da shi cikin biyayyar Allah. Kuma mai hankali shine wanda ya yi hisabi ga kansa, kuma ya yi aiki saboda abinda ke zuwa bayan mutuwa. Gajiyayye kuma, Wanda ya biye wa son zuciyarsa, sai kuma ya kwallafa wa Allah buri.

Idan (dama ta zo maka), isarka ta busa, to ka ribace ta
Domin kowane abu yana da lokacin natsawa.

Kuma kada ka gafala, ga barin aikin kyautatawa a cikinsa
domin baka san lokacin da damarka zata yanke ba 

Ya ku bayin Allah
Lallai kun yi bankwana da watan azumi, wato lokacin falala da da'a da samun gafara, saidai bamu san wanene aka karbi ayyukansa a cikinmu ba, balle mu masa barka, wanene kuma aka mayar da nasa, balle mu masa ta'aziya, Allah ya karbi ayyukanku na da'a, kuma ya gafarta zunubanku, kuma ya ninninka muku lada.

Sannan ku daidaitu akan addinin Allah, ku yi aiki domin karin kusanci zuwa gare shi, saboda tabbatuwa akan da'a yana daga alamomin karbuwar aiki, kuma bawa bai kusanci Allah da komai ba, wanda yafi soyuwa a gare shi fiye da wanda ya farlanta shi akansa, kuma bawa ba zai gushe ba, yana kusantar Allah da nafilfili face Allah ya so, shi. Kuma duk wanda ya kusanci Allah da kamar taki daya, to Allah zai kusance shi da kamar zira'i, kuma wanda ya kusance shi da kamar zira'i, to Allah zai kusance shi da kamar tsawon hannu biyu. Wanda ya je wa Allah yana tafiya, to Allah zai je masa yana sauri.
Sai ku kiyaye farillai, kuma kada ku kaurace wa Alkur'ani, kuma ku rika kwadayin sallolin dare, da azumin yini, saboda an ruwaito daga Sufyan bn Abdullahi As-Sakafiy, ya ce: Na ce wa Manzon Allah, Ka gaya min wata magana a cikin Musulunci wanda ba zan tambayi wani a bayanka ba? Ya ce: "Ka ce: Na yi imani da Allah sannan ka daidaitu".

Kuma lallai yana daga shiriyar Annabinku, azumtar yini shida a cikin watan Shawwal, saboda an ruwaito daga Abu-Ayyub Al'ansariy –Allah ya kara yarda a gare shi- lallai shi ya bada hadisi cewa, lallai Manzon Allah –sallal Lahu alaihi wa sallama- ya ce: "Wanda ya yi azumin watan Ramadana, sa'annan ya biyar musu da guda shida a cikin watan Shawwal, to ya kasance kamar azumin shekara".
Ma'anar wannan shine: Yayin da kyakkyawa aiki ana ninnika shi da kwatankwacinsa goma, to azumtar watan Ramadana zai kasance kamar azumtar watanni guda goma ne, shi kuma azumtar kwanaki shida na Shawwal kamar azumtar watanni biyu, wannan kuma shine daidai da azumtar kwanakin shekara gaba daya.

Ya ku taron Musulmai…
Lokaci kamar dukiya ne, kowanne daga cikinsu wajibi ne ayi kwadayin kiyaye shi, da tattali wajen sarrafa shi da gudanar da lamarinsa.
Kuma idan dukiya za a iya tattara ta, a taskance ta, tare da bunkasa ta, to lallai lokaci lamarinsa ba haka ya ke ba; saboda kowace lahaza da dakika idan ta tafi, to ba za ta dawo gare ka ba, har abada, koda ka kashe dukkan abinda ke bayan kasa gaba daya.
To, idan ya kasance zamani an kaddara masa wani lokaci ayyananne, kuma iyakantacce, wanda ba zai yiwu a gabato da shi ba, ko a jinkirta shi, sai kimarsa -wato lokaci- ta kasance cikin kyautata amfani da shi = to ya wajaba ga kowane Mutum ya kiyaye lokacinsa, ya yi amfani da shi ta hanyar da ta fi kyau, kuma kada ya yi sakaci akan wani abu daga cikinsa; kadan ne ko mai yawa.
Kuma domin Mutum ya kiyaye lokacin, dole ne ya san a ina yake tafiyar da lokacin? Da kuma yadda yake gudanar da shi?
Sai ku saurara!
Lallai mafi girman abinda aka tafiyar da lokaci a cikinsa, kuma mafi daukakansu shine, cikin yin biyayya ga Allah Mabuwayi da daukaka.
Kuma duk zamanin ko lokaci, wanda ka tafiyar da shi cikin wannan biyayyar to baza ka taba nadama a gare shi ba, har abada.

Ya ku bayin Allah…
Rayuwa 'yar kadan ce, zamani kuma gajere ne, kuma duk abinda ya shige ya shige, duk kuma abinda zai zo to mai zuwa ne. kuma rayuwa gaba dayanta lokacin yin biyayya ga Allah ne, kuma babu wata dama ta yin sakaci a cikinta, kuma dukkan rayuwa lokaci ne na jarabtar bayi, don haka babu damar kakkautawa ko jira. Kuma da wannan rayuwar gajeriya Mutum ka iya sayan tabbata madawwamiya a cikin Aljannoni, da wanzuwa wanda ba zai yanke ba, a cikin wani zamani.
Ta daya fiskar kuma, lallai duk wanda ya yi sakaci a rayuwarsa, to lallai zai auka cikin halaka da hasara.
Don haka, Ya dace mai hankali ya san kimar rayuwarsa, kuma ya yi dubi ga ransa cikin lamarinsa, sai ya ribaci abinda ba zai yiwu a risko shi ba, wanda kuma sau dayawa cikin tozarta shi ne, halakar bawa take.

Ya ku taron Musulmai…
Lallai lokacin hutu na bazara da kuke rayuwa a cikinsa wata dama ce ta hutar da jiki, da kuma kokarin sauke wasu hakkoki da yin abinda ya kubuce, da yin guzuri domin lokacin da ake fiskanta na kusa da na nesa. Saboda ba ana bada hutu ba ne, domin a wofintar da hakkoki na wajibai, da tozarta su, da dulmuya cikin sha'awowi, da kakkara dorin doriyar aiyuka, da nauyaya kafadu da laftun ayyuka ko kakkara su a rayuwa.
Sai ku ji tsoron Allah a lamarin iyalanku da 'ya'yanku, kuma ku tarbiyantar da su akan kwadayin kiyaye lokaci, da amfani da shi cikin abubuwa masu amfani, na ilimi da aiki, ta fiskar neman halal, ko aikin da'a da bautar Ma'abucin girma, wannan kuma ita ce tarbiyyar Mazaje.

Kuma lallai tarbiyyar matasa akan tuntsurar da lokuta da damammaki, ya kan koyar da su tozarta hakkoki da wajibai, da gazawa wajen daukar amanoni da nauyin al'umma, kuma yana koyar da su dabi'ar ko-oho, da kasa fiskantar matakan rayuwa.
Shi kuma faraga da rashin aikin yi zai kai yara ga aukawa cikin hatsarin fitintinu, da soye-soyen zuciya, da karkata, da bala'oi.

Ya ku bayin Allah…
Lallai ne Allah zai muku tambaya kan lokutanku na rayuwa; da cewa, ga aikata me, kuka tafiyar da su? Saboda an ruwaito daga Abu-Barzatah Al'aslamiy –Allah ya kara yarda a gare shi- ya ce: Manzon Allah –sallal Lahu alaihi wa sallama- ya ce: "Duga-dugan bawa a ranar Alkiyama ba za su gushe ba, face an tambaye shi kan abubuwa guda hudu; sai an tambaye shi kan rayuwarsa akan me ya salwantar da ita, da iliminsa; me ya aikata da shi, da dukiyarsa ta yaya ya same ta, kuma ga me ya ciyar da ita, da tambaya kan jikinsa a me ya tsufar da shi?".

Kuma idan Mutum ya iso wurin hisabi, sannan ya kafu tsaye akan kafofinsa babu takalmi, kuma babu tufafi, (a gaba ga Ubangijinsa) babu shamaki, yana jiran a tambaye shi, kuma yana shirin bada amsa = Sai aka tambaye shi kan rayuwarsa a me ya tafiyar da ita? Da samartakarsa a me ya salwantar da ita?
Wayyo Allah! Me yafi wannan lamari girma, kuma me yafi wannan musiba tsanani?

Wajibi ne kowanne daga cikinmu ya tambayi kansa, idan aka jefo masa wannan tambayar, me zai darsu a zuciyarsa?
Kuma wane aiki ya tanada tsawon samartakarsa, da kuma rayuwarsa? Kuma me ya shirya don ya zama amsa?

Sai ku yi tanadin amsa –Ya ku bayin Allah- ga wannan tambayar, kuma amsar ta zama daidai.

Allah ya sanya mu da ku, "daga cikin wadanda suke jin zance, sai su bi mafi kyansa, domin wadannan sune wadanda Allah ya shiryar, kuma wadannan sune ma'abuta hankali" [Zumar: 18].

,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,

HUDUBA TA BIYU
Yabo ya tabbata ga Allah, kuma ya isar,
Salati da sallama su kara tabbata ga bayinSa wadanda ya zaba.

Ya ku bayin Allah…
Lallai mai hankali ba zai yarda ya tozarta dakikon numfashinsa ba, alhalin rayuwarsa tana raguwa, ya tozarta su wuce kara zube, ba a cikin lamarin Duniya ko lamarin lahirarsa ba.
Kuma lallai samun lokaci da faraga ni'ima ce, idan aka kyautata moransa, azaba ce kuma idan aka tozarta aiki da shi, saboda an ruwaito daga Abdullahi bn Abbas –Allah ya kara yarda a gare su- ya ce: Annabi –sallal Lahu alaihi wa sallama- ya ce: "Ni'imomi guda biyu an rinjayi Mutane dayawa akansu; sune lafiya da samun lokaci".
Don haka, almubazzarantar da lokatai, bugun hanci ne da tawaya cikin addini, kuma rauni ne da wauta cikin hankula, wanda aka jarrabi Mutane dayawa da aikata shi;
Sai ku ji tsoron Allah akan rayukanku da abin kiyonku, kuma ku ribaci damammaki, kuma ku yi kwadayin riko da su, domin an ruwaito daga Abdullahi bn Abbas –Allah ya kara yarda a gare su- ya ce: Manzon Allah –sallal Lahu alaihi wa sallama- ya fada wa wani Mutum alhalin yana masa wa'azi: "Ka ribaci abu biyar gabanin abubuwa biyar; samartakarka gabanin tsufanka, da lafiyarka gabanin cutarka, da wadacinka gabanin talaucinka, da faragarka gabanin shagaltuwarka, da rayuwarka gabanin mutuwarka".

Ya ku masu yin tarbiyya…
Lallai ne babu wani kunci cikin moriyar jin dadi, da shakatawa, da debe kewa, da neman sararawa, matukar babu ketare iyaka, ko aikata abin ki a cikinsa, ko tozarta hakkoki da wajibai, domin hakan yana cikin jin dadi da abubuwa na halal, kuma a cikin hakan akwai sake jaddada karfin jiki, da nashadantar da rai. Saidai kuma ba tare da an tuntsurar ko an yi almubazzarancin lokuta masu tsada ba, kuma ba tare da an tsananta cikin wasa ko an zurfafa cikin gafala ba, domin al'ummar musulunci tana da matsanancin bukatar karfi da lokutan 'ya'yanta, sai ku tsakaita, kuma ku kwatanta.

Bayan haka, Ya ku taron Musulmai…
Lallai abinda ke aukuwa tsakanin Musulmai na sabani da gujewa-juna, da fadace-fadace, da soke-soke, yana daga cikin manyan ababen bakin ciki, da musibu masu daga hankali, da fitintinu mafiya tsanani, da manyan ababen da suke janyo wa zukata bacin rai.
Kuma lallai tsayar da lamarin zuban jinin Musulmai, da kiyaye mutuncinsu da dukiyoyinsu, yana daga cikin manya-manyan manufofin Musulunci, da tabbatattun abubuwa a cikin addini mikakke, kuma wannan shine lafiyayyun hankali suke hukuntawa.
Kuma lallai Duniyar Musulmai ta zura ido, tana fatan samun zaman lafiya tsakanin 'yan'uwanmu na kasar Afganistan, kuma tana maraba da samun sulhu a tsakaninsu, bayan abinda ya sauka akansu na bone da yakuka suka haifar, da kuma fadace-fadace, da rabuwar kai da jayayya, wanda a cikinsu yara da mata suka dandani kudarsu. Har wadanda basu ji, ko suka gani ba, suke ta neman taimakon Majibinci Madaukaki.

Taki ba komai ba ne, sai abinda kuka sani, kuma kuka dandana
Kuma shi a wurinku, ba labari ba ne na gaibu

Ya ku 'yan'uwa Mutanen Afganistan…
Yin sulhu alheri ne, sai ku ji tsoron Allah, ku yi sulhu, ku yi afuwa ku yi yafiya, "Lallai Muminai 'yan'uwa ne; sai ku yi sulhu tsakanin 'yan'uwanku" [Hujurat: 10].
"kuma wanda ya yi hakuri, kuma ya gafarta, lallai wannan yana daga manyan lamura" [Shura: 43].
Don haka, kyale wasu maslahohin, domin tsayar da zuban jinin Musulmai yana da falala mai girma, kuma maslaha ce babba, kuma karfin hali ne da gwarzantaka wanda ya kai makura.
Sai ku tsayar da shekar da jinin jama'arku da al'ummarku, kuma ku yi sulhu abinda ke tsakaninku, kuma ku taimaki junanku akan biyayyar Allah da takawa, kuma kada ku taimaki wani akan sabo da ketare iyaka.

Allah ya hade abinda ya wargaje a tsakaninku, ya daidaita kalmarku, ya kawo sulhu a tsakaninku, ya daidaita tsakanin zukatanku, kuma ya kashe wutar fitina da zafin kai, wanda da ta kunnu a kasarku.

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...