2015/09/23

ADDU'OIN MAHAJJACI A FILIN ARAFAH DA BAYANIN AIYUKAN WANNAN YININ (09 / zulhijjah)

ADDU'OI A YININ ARAFAH     DA AYYUKANSA GA MAHAJJACI
Bayan fudowar rana a yinin arafah mahajjaci zai nufi filin arafah daga minah, kuma sunnah ne mahajjata su fara sauka a filin namirah (da yake iyaka da filin arafah) har zuwa rana ta yi zawali, gabanin su shiga cikin filin arafah, idan hakan ya sauqaqa a gare su, saboda Annabi (r) ya aikata hakan.
Idan rana ta yi zawali sunnah ne ga limami ko na'ibinsa ya yi huxuba ga mutane; huxubar da ta dace da halin da ake ciki, yana mai bayyana wa mahajjata aiyukan da aka shar'anta musu aikata su a wannan yinin, da kuma kwanakin da suke bayansa, ya kuma umurce su a cikinta da taqawar Allah da tauhidinsa, da yi masa ikhlasi (tsantsanta ibada a gare shi, shi kaxai) a cikin dukkan aiyuka, ya kuma hane su aikata abubuwan da Allah ya haramta musu, an so ya yi musu wasiyya a cikinta da cewa su yi riqo da littafin Allah (alqur'ani) da kuma sunnar Annabi (r) da yin hukunci da su, tare da neman hukuncinsu cikin dukkan lammura, suna masu koyi da Annabi (r) cikin wannan dukkansa. Bayan kamala yin huxuba kuma sai su sallaci azahar da la'asar, qasaru (raka'a bibbiyu), tare da haxe su (aikata su) a lokacin sallar farko (azahar), da kiran sallah guda xaya, tare da yin iqamah guda biyu, saboda haka Annabi (r) ya aikata, kamar yadda Imam Muslim ya ruwaito hakan a cikin hadisin Jabir (ra) mai tsayi([1]).
Daga nan, sai mutane su tsaya a arafah, kuma filin arafah dukkansa wurin tsayuwa ne in banda wurin da ake kiransa BAXANU URANAH. Kuma mustahabbi ne mahajjaci ya fiskanci alqiblah tare da dutsen da ake kiransa JABALUR RAHMAH idan hakan ya sauqaqa masa, idan kuma hakan bai sauwaqa ba to sai ya fiskanci alqiblar kawai, koda kuwa bai fiskanci dutsen ba.
Kuma mustahabbi ne ga mahajjaci a wannan matsaya (arafah) ya yi iya qoqarinsa wajen ambaton Allah (سبحانه وتعالى) da roqonsa, tare kuma da kankan-da-kai a gare shi, kuma zai xaga hannayensa biyu a yayin addu'a, kuma idan da zai yi talbiyyah ko ya karanta wani abu na alqur'ani a wannan yinin to hakan ya yi kyau,  an kuma sunnanta masa yawaita faxin: LA ILAHA ILLAL LAHU WAHDAHU LA SHARIKA LAHU LAHUL MULKU WA LAHUL HAMDU YUHYIY WA YUMIYTU WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN QADIIR, saboda abun da aka ruwaito daga Annabi (r) cewa:
«خَيْرُ الدُّعَاءِ دُعَاءُ يَوْمِ عَرَفَةَ، وَخَيْرُ مَا قُلْتُ أَنَا وَالنَّبِيُّونَ مِنْ قَبْلِي: لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الحَمْدُ وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ».
Ma'ana: "Mafi alherin addu'a shine addu'an yinin arafah, kuma mafi alherin abinda na faxa ni da annabawa a gabanina shine: LA ILAHA ILLAL LAHU WAHDAHU LA SHARIKA LAHU LAHUL MULKU WA LAHUL HAMDU WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN QADIIR"([2]), Kuma ya inganta daga gare shi (r) lallai ya ce:
«أَحَبُّ الْكَلَامِ إِلَى اللهِ أَرْبَعٌ: سُبْحَانَ اللهِ، وَالْحَمْدُ لِلَّهِ، وَلَا إِلَهَ إِلَّا اللهُ، وَاللهُ أَكْبَر».
Ma'ana: "Mafi soyuwan magana a wajen Allah guda huxu ne; SUBHANAL LAHI, WAL HAMDU LIL LAHI, WA LA ILAHA ILLAL LAHU, WALLAHU AKBAR"([3]).
            Don haka; Yana da kyau a yawaita faxin wannan zikirin tare da maimaita shi cikin nitsuwar zuci, da halarto da tunani. Kuma ya dace (ga mahajjaci) ya yawaita yin sauran zikirori da addu'oin da suka zo a shari'a cewa ana yinsu a kowani lokaci, musamman kuma a wannan bagire da wannan yini mai girma; wato yinin arafah, kuma yana da kyau mutum ya zavi gamemmu daga cikin addu'oi da zikirori, Daga cikinsu:
سُبْحَانَ اللهِ وَبِحَمْدِهِ، سُبْحَانَ اللهِ الْعَظِيم، لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظَّالِمِينَ الأنبياء: 87
SUBHANAL LAHI WABI HAMDIH, SUBHANAL LAHIL AZIIM. LA ILAHA ILLA ANTA SUBHANAKA INNIY KUNTU MINAZ ZALIMINA.
            Ma'ana: "Tsarki ya tabbata ga Allah, kuma godiya tasa ce, tsarki ya tabbata ga Allah mai girma. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, tsarki ya tabbata maka, lallai ni na kasance daga cikin azzalumai".
«لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ، وَلَا نَعْبُدُ إِلَّا إِيَّاهُ، لَهُ النِّعْمَةُ، وَلَهُ الْفَضْلُ، وَلَهُ الثَّنَاءُ الْحَسَنُ، لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ، مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ وَلَوْ كَرِهَ الْكَافِرُونَ».
LA ILAHA ILLAL LAHU, WALA NA'ABUDU ILLA IYYAHU, LAHUN NI'IMAH, WA LAHUL FADLU, WA LAHUS SANA'UL HASAN, LA ILAHA ILLAL LAHU MUKHLISINA LAHUD DINA WA LAU KARIHAL KAFIRUUNA.
            Ma'ana: "Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma bama bauta ga wani sai kai, ni'ima tasa ce, kuma falala tasa ce, kuma yabo mai kyau nasa ne, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, muna masu tsarkake masa addini, koda kafirai sun qi".
«لَا حَوْلَ وَلَا قُوَّةَ إِلَّا بِاللَّهِ».
LA HAULA WALA KUWWATA ILLA BIL LAHI.
            Bawa bashi da dabarar barin savo, bashi da qarfin iya biyayya ga Allah, sai ya samu taimakon Allah.
ﯜ  ﯝ  ﯞ  ﯟ   ﯠ  ﯡ  ﯢ  ﯣ  ﯤ  ﯥ  ﯦ  البقرة: ٢٠١
RABBANA ATINA FID-DUNYAH HASANATAN, WA FIL AKHIRATI HASANATAN, WA QINA AZABAN NAARI.
            Ma'ana: "Ya Ubangijinmu ka bamu abu mai kyau a duniya, a lahirama mai kyau, ka kare mu daga azabar wuta".
«اللهُمَّ أَصْلِحْ لِي دِينِي الَّذِي هُوَ عِصْمَةُ أَمْرِي، وَأَصْلِحْ لِي دُنْيَايَ الَّتِي فِيهَا مَعَاشِي، وَأَصْلِحْ لِي آخِرَتِي الَّتِي فِيهَا مَعَادِي، وَاجْعَلِ الْحَيَاةَ زِيَادَةً لِي فِي كُلِّ خَيْرٍ، وَاجْعَلِ الْمَوْتَ رَاحَةً لِي مِنْ كُلِّ شَرٍّ».
ALLAHUMMA AS-LIH LIY DIYNIY AL-LAZIY HUWA ISMATU AMRIY, WA ASLIH LIY DUNYAY AL-LATIY FIYHA MA'ASHIY, WA ASLIH LIY AKHIRATIY AL-LATIY FIYHA MA'ADIY, WAJ'ALIL HAYATA ZIYADATAN LIY FIY KULLI KHAIR, WAJ'ALIL MAUTA RAHATAN LIY MIN KULLI SHARR.
            Ma'ana: "Ya Allah ka gyara min addinina wanda shine gyaran lamarina, ka kuma gyara mini duniyata wacce a cikinta rayuwata ta ke, ka kuma gyara min lahirata wacce zuwa gare ta makomata ta ke, ka sanya rayuwa ta zama qaruwa ce a gare ni cikin dukkan alheri, mutuwa kuma ta zamto hutu daga aikata dukkan sharri".
أَعُوذُ بِاللَّه «مِنْ جَهْدِ الْبَلَاءِ، وَدَرَكِ الشَّقَاءِ، وَسُوءِ الْقَضَاءِ، وَشَمَاتَةِ الْأَعْدَاءِ».
A'UZU BILLAHI MIN JAHDIL BALA'I, WA DARAKISH SHAQA'I, WA SUW'IL QADA'I, WA SHAMATATIL A'ADA'I.
            Ma'ana: "Ina neman tsarin Allah kan wahalhalun bala'i, da kuma kan riskar wahala, da mummunar qaddara, da dariyar qeta daga maqiya".
«اللَّهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنَ الْهَمِّ وَالْحَزَنِ، وَالْعَجْزِ وَالْكَسَلِ، وَالْجُبْنِ وَالْبُخْلِ، ومِنَ الْمَأْثَمِ وَالْمَغْرَم، وَمِن ضَلَعِ الدَّيْنِ وَقَهْرِ الرِّجَالِ.   اللهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنَ الْبَرَصِ وَالْجُنُونِ وَالْجُذَامِ وَسَيِّءِ الأَسْقَام».
ALLAHUMMA INNIY A'UZU BIKA MINAL HAMMI WAL HAZAN, WAL AJZI WAL KASLI, WAL JUBNI WAL BUKHLI, WA DALA'ID DAINI, WA GALABATIR RIJAALI.
ALLAHUMMA INNIY A'UZU BIKA MINAL BARASI, WAL JUNUNI, WAL JUZAAMI, WA SAYYI'IL ASQAAMI.
            Ma'ana: "Ya Allah lallai ni ina neman tsarinka daga baqin ciki, da gajiyawa da kasala, da tsoro da rowa, da kuma savo, da bashi, da kuma nauyinsa (bashi), da rinjayen mazaje.  Ya Allah ka tsare ni daga ciyon kuturta, da hauka, da kuturta mai yanke yatsu, da kuma munanan cutuka".
«اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الْعَفْوَ وَالْعَافِيَةَ، فِي الدُّنْيَا وَالْآخِرَةِ».
ALLAHUMMA INNIY AS'ALUKAL AFWA WAL AFIYAH, FID DUNYA WAL AKHIRAH.
Ma'ana: "Ya Allah ina roqonka afuwa da lafiya, a duniya da lahira".
«اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الْعَفْوَ وَالْعَافِيَةَ فِي دِينِي وَدُنْيَايَ وَأَهْلِي وَمَالِي».
ALLAHUMMA INNIY AS'ALUKAL AFWA WAL AFIYAH, FIY DIYNIY, WA DUNYAY, WA AHLIY, WA MALIY.
Ma'ana: "Ya Allah lallai ni ina roqonka afuwa da lafiya, a addinina da duniyata da iyalaina da dukiyata".
«اللَّهُمَّ اسْتُرْ عَوْرَاتِي، وَآمِنْ رَوْعَاتِي، اللَّهُمَّ احْفَظْنِي مِنْ بَيْنِ يَدَيَّ، وَمِنْ خَلْفِي، وَعَنْ يَمِينِي، وَعَنْ شِمَالِي، وَمِنْ فَوْقِي، وَأَعُوذُ _ بِعَظَمَتِكَ _ أَنْ أُغْتَالَ مِنْ تَحْتِي».
ALLAHUMMA US-TUR AURAATIY, WA AAMIN RAU'AATIY, ALLAHUMMA IHFAZNIY MIN BAINI YADAYYA WA MIN KHALFIY, WA AN YAMIYNIY, WA AN SHIMALIY, WA MIN FAUQIY, WA A'UZU –BI AZAMATIKA- AN UGTALA MIN TAHTIY.
Ma'ana: "Ya Allah ka suturce min al'aurata, ka amintar da tsorona, Ya Allah ka bani kariya ta gaba gare ni da kuma ta bayana, da ta damana da ta hagun xina, da ta samana, kuma ina neman tsari –da girman Allah- kar a halaka ni ta qasana (kamun qasa ko makamancin haka)".
«اللَّهُمَّ اغْفِرْ لِي خَطِيئَتِي وَجَهْلِي، وَإِسْرَافِي فِي أَمْرِي، وَمَا أَنْتَ أَعْلَمُ بِهِ مِنِّي».
ALLAHUMMA IGFIR LIY KHAXIY'ATIY WA JAHLIY, WA ISRAFIY FIY AMRIY, WAMA ANTA A'ALAMU BIHI MINNIY.
            Ma'ana: "Ya Allah ka gafarta mini kurakuraina da jahilcina, da wuce iyakata a cikin lamura, da abinda kaine mafi saninsa fiye da ni".
اللَّهُمَّ اغْفِرْ لِي جِدّي وَهَزْلِي، وخَطَئِي وَعَمْدِي، وَكُلُّ ذَلِكَ عِنْدِي.
ALLAHUMMA IGFIR LIY JIDDIY, WA HAZLIY, WA KHAXA'IY WA AMDIY, WA KULLU ZALIKA INDIY.
            Ma'ana: "Ya Allah ka gafarta min gaskena da wargina, da kuskurena da gangancina, saboda akwai dukkan hakan daga wajena".
"اللَّهُمَّ اغْفِرْ لِي مَا قَدَّمْتُ وَمَا أَخَّرْتُ، وَمَا أَسْرَرْتُ وَمَا أَعْلَنْتُ، وَمَا أَنْتَ أَعْلَمُ بِهِ مِنِّي، أَنْتَ الْمُقَدِّمُ وَأَنْتَ الْمُؤَخِّرُ، وَأَنْتَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ".
ALLAHUMMA IGFIR LIY MA QADDAMTU WAMA AKKHARTU, WAMA ASRARTU WAMA A'ALANTU, WAMA ANTA A'ALAMU BIHI MINNIY, ANTAL MUQADDIMU WA ANTAL MU'AKKHIRU, WA ANTA ALA KULLI SHAI'IN QADIIR.
            Ma'ana: "Ya Allah ka gafarta mini abinda na gabatar, da abinda na jinkirtar, da abinda na asirta (voye) da abinda na bayyanar, da kuma abinda kaine mafi saninsa fiye da ni, kai ne mai gabatarwa, kai ne kuma mai jinkirtarwa, kuma kai mai iko ne akan komai".
"اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الثَّبَاتَ فِي الْأَمْرِ، وَالْعَزِيمَةَ عَلَى الرُّشْدِ، وَأَسْأَلُكَ شُكْرَ نِعْمَتِكَ، وَحُسْنَ عِبَادَتِكَ، وَأَسْأَلُكَ قَلْبًا سَلِيمًا، وَلِسَانًا صَادِقًا. وَأَسْأَلُكَ مِنْ خَيْرِ مَا تَعْلَمُ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا تَعْلَمُ، وَأَسْتَغْفِرُكَ لِمَا تَعْلَم، وَأَنْتَ عَلَّامُ الْغُيُوبِ".
ALLAHUMMA INNIY AS'ALUKAS SABATA FIL AMRI, WAL AZIYMATA ALAR RUSHDI, WA AS'ALUKA SHUKRA NI'IMATIKA, WA HUSNA IBADATIKA, WA AS'ALUKA QALBAN SALIYMAN, WA LISANAN SADIQAN, WA AS'ALUKA MIN KHAIRI MA TA'ALAMU, WA A'UZU BIKA MIN SHARRI MA TA'ALAMU, WA ASTAGFIRUKA LIMA TA'ALAMU, WA ANTA ALLAMUL GUYUUB".
            Ma'ana: "Ya Allah lallai ina roqonka tabbatuwa cikin addini, da azama akan shiriya, Ina kuma roqonka godiya ga ni'imominka, da kyautata bauta a gare ka, kuma ina roqon ka bani zuciya kuvutacciya, da harshe mai gaskiya, Ina kuma roqonka alherin abinda ka sani, ina neman tsarinka daga sharrin da ka riga ka sani, ina kuma neman gafararka daga abinda ka sani, kuma kai ne masanin abubuwan da suke fake (voye, na gaibu)".
اللَّهُمَّ رَبَّ النَّبِيِّ مُحَمَّدٍ عليه الصلاة والسلام اغْفِرْ لِي ذَنْبِي، وَأَذْهِبْ غَيْظَ قَلْبِي، وَأَجِرْنِي مِنْ مُضِلاَّتِ الْفِتَنِ مَا أَبْقَيْتَنِي.
ALLAHUMMA RABBAN NABIYYI MUHAMMADIN (ALAIHIS SALATU WAS SALAM), IGFIRLIY ZANBIY, WA AZHIB GAIZA QALBIY, WA AJIRNIY MIN MUDILLATIL FITANI MA ABQAITANIY.
            Ma'ana: "Ya Allah Ubangijin annabi (Muhammadu) tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi, ka gafarta mini zunubina, ka tafiyar da baqin cikin zuciyata, ka kare ni daga fitintinu masu batarwa tsawon lokacin da ka wanzar da ni (a raye)".
اللَّهُمَّ رَبَّ السَّماوَاتِ السَّبْعِ، وَرَبَّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ، رَبَّنَا وَرَبَّ كُلِّ شَيْءٍ، مُنْزِلَ التَّوْرَاةِ وَالإِنْجِيلِ وَالْقُرْآنِ، فَالِقَ الْحَبِّ وَالنَّوَى، لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ، أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ كُلِّ شَيْءٍ أَنْتَ آخِذٌ بِنَاصِيَتِهِ، أَنْتَ الأَوَّلُ لَيْسَ قَبْلَكَ شَيْءٌ، وَأَنْتَ الآخِرُ لَيْسَ بَعْدَكَ شَيْءٌ، وَأَنْتَ الظَّاهِرُ لَيْسَ فَوْقَكَ شَيْءٌ، وَأَنْتَ الْبَاطِنُ لَيْسَ دُونَكَ شَيْءٌ، اقْضِ عَنَّا الدَّيْنَ، وَأَغْنِنَا مِنَ الْفَقْر.
ALLAHUMMA RABBAS SAMAWATIS SABA'I, WA RABBAL ARSHIL AZIIM, RABBANA WA RABBA KULLI SHAI'IN, MUNZILAT TAURATI WAL INJILI WAL QUR'ANI, FALIQAL HABBI WAN NAWAH, LA ILAHA ILLA ANTA, A'UZU BIKA MIN SHARRI KULLI SHAI'IN ANTA AAKHIZUN BI NASIYATIHI, ANTAL AUWALU FA LAISA QABLAKA SHAI'UN, WA ANTAL AAKHIRU FA LAISA BA'ADAKA SHAI'UN, WA ANTAZ ZAHIRU FA LAISA FAUQAKA SHAI'UN, WA ANTAL BAXINU FA LAISA DUNAKA SHAI'UN, IQDI ANNA AD-DAINA WA AGNINA MINAL FAQRI.
            Ma'ana: "Ya Allah Ubangijin sammai guda bakwai, ubangijin al'arshi mai girma, Ubangijinmu kuma Ubangijin komai da kowa, wanda ya sauqar da littafin attaurah da injilah da alqur'ani, kai ka qagi halittar kwayan tsirrai da kwallonsu, Ina neman tsarinka daga dukkan sharri wanda kai ne ka ke riqe da maqyamqyamarsa, Ya Allah kai ne farko; babu wani abu gabaninka, kuma kai ne qarshe; babu wani abu a bayanka, kai ne maxaukaki; babu wani abu a samanka, kai ne kuma iliminka ya game; babu wani abu da ya fice daga iliminka, (ya Allah) ka biya mana bashin da yake kanmu, kuma ka wadatar da mu daga talauci".
«اللَّهُمَّ ائْتِ نَفْسِي تَقْوَاهَا، زَكِّهَا أَنْتَ خَيْرُ مَنْ زَكَّاهَا، أَنْتَ وَلِيُّهَا وَمَوْلَاهَا».
ALLAHUMMA ATI NAFSIY TAQ-WAHA, ZAKKIHA ANTA KHAIRU MAN ZAKKAHA, ANTA WALIYYUHA WA MAULAHA.
            Ma'ana: "Ya Allah ka bawa raina taqawarta, ka tsarkake ta; saboda kaine mafi alherin wanda ya jivinceta kuma masoyinta".
«اللَّهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنَ الْعَجْزِ وَالْكَسَلِ ، وَالْجُبْنِ وَالْهَرَمِ ، وَالْبُخْلِ وَعَذَابِ الْقَبْرِ».
ALLAHUMMA INNIY A'UZU BIKA MINAL AJZI WAL KASALI, WAL JUBNI WAL HARAMI, WAL BUKHLI WA AZABIL QABRI".
            Ma'ana" Ya Allah ina neman tsarinka daga gajiyawa da kasala, da tsoro, da mummunan tsufa, da rowa da kuma azabar qabari".
«اللهُمَّ لَكَ أَسْلَمْتُ، وَبِكَ آمَنْتُ، وَعَلَيْكَ تَوَكَّلْتُ، وَإِلَيْكَ أَنَبْتُ، وَبِكَ خَاصَمْتُ، اللهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِعِزَّتِكَ لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ أَنْ تُضِلَّنِي، أَنْتَ الْحَيُّ الَّذِي لَا يَمُوتُ، وَالْجِنُّ وَالْإِنْسُ يَمُوتُونَ».
ALLAHUMMA LAKA ASLAMTU, WA BIKA AMANTU, WA ALAIKA TAWAKKALTU, WA ILAIKA ANABTU, WA BIKA KHASAMTU, ALLAHUMMA INNIY A'UZU BI IZZATIKA, LA ILAHA ILLA ANTA, AN TUDILLANIY, ANTAL HAYYU ALLAZIY LA YAMUTU, WAL JINNU WAL INSU YAMUUTUUNA.
            Ma'ana: "Ya Allah a gare ka kawai na miqa wuya, kuma da kai ne kawai na yi imani, akanka kaxai na dogara, zuwa gare ka na mayar da lamarina, don kai kawai na ke husuma, Ya Allah lallai ina neman tsarinka da buwayarka, babu abin bautawa da gaskiya sai kai; kada ka vatar da ni, kai ne rayayyen da baya mutuwa, da mutane da aljanu duk suna mutuwa".
«اللهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنْ عِلْمٍ لَا يَنْفَعُ، وَمِنْ قَلْبٍ لَا يَخْشَعُ، وَمِنْ نَفْسٍ لَا تَشْبَعُ، وَمِنْ دَعْوَةٍ لَا يُسْتَجَابُ لَهَا».
ALLAHUMMA INNIY A'UZU BIKA MIN ILMIN LA YANFA'U, WA MIN QALBIN LA YAKH'SHA'U, WA MIN NAFSIN LA TASHBA'U, WA MIN DA'AWATIN LA YUSTAJAABU LAHA.
            Ma'ana: "Ya Allah lallai ina neman tsarinka daga samun ilimin da bashi da amfani, da kuma zuciya da bata samun kushu'i (tsoron Allah), da rai da ba ta koshi, da kuma addu'ar da ba a amsa mata".
«اللَّهُمَّ جَنِّبْنِي مُنْكَرَاتِ الْأَخْلَاقِ، وَالْأَهْوَاءِ، وَالْأَدْوَاءِ».
ALLAHUMMA JANNIBNIY MUNKARATIL AKHLAQI, WAL AHWA'I, WAL ADWA'I.
            Ma'ana: "Ya Allah ka nisantar da ni da munanan halayya, da son zuciya, da cutuka".
«اللَّهُمَّ أَلْهِمْنِي رُشْدِي، وَأَعِذْنِي مِنْ شَرِّ نَفْسِي».
ALLAHUMMA AL-HIMNIY RUSHDIY, WA A'IZNIY MIN SHARRI NAFSIY.
            Ma'ana: "Ya Allah ka min ilhamar shiriyata, ka kuma kare ni daga sharrin kaina".
«اللَّهُمَّ اكْفِنِي بِحَلَالِكَ عَنْ حَرَامِكَ، وَأَغْنِنِي بِفَضْلِكَ عَمَّنْ سِوَاكَ».
ALLAHUMMA IKFINIY BI HALALIKA AN HARAMIKA, WA AGNINIY BI FADLIKA AN MAN SIWAKA.
            Ma'ana: "Ya Allah ka wadatar da ni da halal xinka, ga barin haramiyarka, ka kuma wadatar da ni da falalarka daga wanda ba kai ba".
«اللهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الْهُدَى وَالتُّقَى وَالْعَفَافَ وَالْغِنَى».
ALLAHUMMA INNIY AS'ALUKAL HUDAH, WAT TUQAH, WAL AFAFA, WAL GINAH.
            Ma'ana: "Ya Allah lallai ina roqonka shiriya, da taqawa, da kamewa, da kuma wadaci".
«اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الْهُدَى وَالسَّدَاد».
ALLAHUMMA INNIY AS'ALUKAL HUDAH WAS SADAD.
            Ma'ana: "Ya Allah ina roqonka da ka bani shiriya da dacewa".
«اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ مِنَ الْخَيْرِ كُلِّهِ؛ عَاجِلِهِ وَآجِلِهِ، مَا عَلِمْتُ مِنْهُ وَمَا لَمْ أَعْلَمْ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنَ الشَّرِّ كُلِّهِ؛ عَاجِلِهِ وَآَجِلِهِ، مَا عَلِمْتُ مِنْهُ، وَمَا لَمْ أَعْلَمْ.   اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ مِنْ خَيْرِ مَا سَأَلَكَ عَبْدُكَ وَنَبِيُّكَ مُحَمَّدٌ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا استعَاذَ مِنْهُ عَبْدُكَ وَنَبِيُّكَ مُحَمَّدٌ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ.   اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الْجَنَّةَ وَمَا قَرَّبَ إِلَيْهَا مِنْ قَوْلٍ أَوْ عَمَلٍ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنَ النَّارِ وَمَا قَرَّبَ إِلَيْهَا مِنْ قَوْلٍ أَوْ عَمَلٍ، وَأَسْأَلُكَ أَنْ تَجْعَلَ كُلَّ قَضَاءٍ تَقْضِيهِ لِي خَيْرًا».
ALLAHUMMA INNIY AS'ALUKA MINAL KHAIRI KULLIHI AJILIHI WA AJILIHI, MA ALIMTU MINHU WAMA LAM A'ALAM, WA A'UZU BIKA MINASH SHARRI KULLIHI; AJILIHI WA AJILIHI, MA ALIMTU MINHU WAMA LAM A'ALAM.
ALLAHUMMA INNIY AS'ALUKA MIN KHAIRI MA SA'ALAKA ABDUKA WA NABIYYUKA MUHAMMADUN (r), WA A'UZU BIKA MIN SHARRI MA ISTA'AZA MINHU ABDUKA WA NABIYYUKA MUHAMMADUN (r).
ALLAHUMMA INNIY AS'ALUKAL JANNATA WAMA QARRABA ILAIHA MIN QAULIN AU AMALIN, WA A'UZU BIKA MINAN NAARI WAMA QARRABA ILAIHA MIN QAULIN AU AMALIN. WA AS'ALUKA AN TAJ'ALA KULLA QADA'IN QADAITAHU LIY KHAIRAH.
            Ma'ana: "Ya Allah ina roqonka alkhairi dukkansa; na gaggawa daga cikinsa da na nesa, wanda na sani daga ciki da wanda ban sani ba. Ina kuma neman tsarinka sharri dukkansa; na gaggawa daga cikinsa, da na nesa, wanda na sani daga ciki da wanda ban sani ba.
Ya Allah ina roqonka duk abinda bawanka kuma annabinka Muhammadu (r) ya tava roqonka, Ina kuma neman tsarinka daga abinda bawanka kuma annabinka Muhammadu (r) ya tava neman tsarinka.
Ya Allah ina roqon aljannah da duk abinda yake kusantarwa zuwa gare ta na zance ko aiki, Ina kuma neman tsarinka daga wuta da duk abinda yake kusantarwa zuwa gare ta na zance ko aiki. Kuma ina roqon da ka sanya dukkan abinda ka qaddara min ya zamto alkhairi a gare ni.
«لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ، وَلَهُ الْحَمْدُ يُحْيِي وَيُمِيتُ وَهُوَ حَيٌّ لَا يَمُوتُ، بِيَدِهِ الْخَيْرُ، وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِير. سُبْحَانَ اللَّهِ، والْحَمْدُ لِلَّهِ، وَاللَّهُ أَكْبَرُ، وَلَا حَوْلَ وَلَا قُوَّةَ إِلَّا بِاللَّهِ العلي العظيم».
LA ILA ILLAL LAHU; WAHDAHU LA SHARIKA LAHU, LAHUL MULKU WA LAHUL HAMDU, YUHYIY WA YUMIYTU, WA HUWA HAYYUN LA YAMUUTU, BIYADIHIL KHAIRU WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN QADIIR.
SUBHANAL LAHI, WAL HAMDU  LILLAHI, WAL LAHU AKBAR, WALA HAULA WALA QUWWATA ILLA BIL LAHIL AL' ALIYYUL AZIIM.
            Ma'ana: "Babu wanda ya cancanci ayi masa bauta sai Allah; shi kaxai ya ke; bashi da abokin tarayya, mulki nasa ne, godiya itama tasa ce, yana rayarwa kuma yana kashewa, shi kuma rayayye ne da baya mutuwa, a hannunsa alheri ya ke, kuma lallai shi mai iko ne akan komai. Tsarki ya tabbata ga Allah, godiya itama ta Allah ce, Allah shine mafi girma, babu dabara babu qarfi (ga bawa), sai in ya haxa da Allah".
«اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، فِي الْعَالَمِين إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَـارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، فِي الْعَالَمِين إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيد».
"ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMADIN WA ALA ALI MUHAMMADIN, KAMA SALLAITA ALA AALI IBRAHIMA WA ALA AALI IBRAHIMA FIL AALAMINA INNAKA HAMIDUN MAJIID.
ALLAHUMMA BARIK ALA MUHAMMADIN WA ALA AALI MUHAMMADIN, KAMA BARAKTA ALA IBRAHIMA WA ALA AALI IBRAHIMA FIL AALAMINA INNAKA HAMIDUN MAJIID".
            Ma'ana: "Ya Allah ka yi qarin salati ga annabi Muhammad, da iyalan annabi Muhammad, kamar yadda ka yi salati ga annabi Ibrahima da kuma iyalan annabi Ibrahima, lallai kai a cikin halittu Abun yabo ne Mai girma.  Ya Allah ka yi qarin albarka ga annabi Muhammadu, da iyalan annabi Muhammad, kamar yadda ka yi albarka wa annabi Ibrahima da kuma iyalan annabi Ibrahima, lallai kai a cikin halittu Abun yabo ne Mai girma".
ﯜ  ﯝ  ﯞ  ﯟ   ﯠ  ﯡ  ﯢ  ﯣ  ﯤ  ﯥ  ﯦ  البقرة: ٢٠١
RABBANA ATINA FID DUNYAH HASANATAN, WA FIL AKHIRATI HASANATAN, WA QINA AZABAN NAAR.
            Ma'ana: "Ya Ubangijinmu ka bamu mai kyau a duniya, a lahirama mai kyau, ka kuma kare mu daga azabar wuta".
Kuma mustahabbi ne a wannan matsaya mai girma (filin arafah) mahajjaci ya yi ta maimaita abinda ya gabata na zikirori da addu'oi, da kuma makamantan haka waxanda su ke xauke da irin ma'anoninsu, tare da yawaita yin salati ga Annabin rahama (r), kuma an so mahajjaci ya yi ta naci wajen addu'a da dogewa akan naciyar, yana mai roqon Ubangijinsa alherin duniya da kuma na lahira.
Kuma Annabi (r) ya kasance idan yana roqon Allah ya kan maimaita buqatarsa har sau uku, don haka; ya dace a yi koyi da shi akan haka.
Ana so musulmi a wannan matsaya (filin arafah) ya qanqantar da kansa ga Ubangijinsa, yana mai yi masa tawali'u, tare da nuna karayar zuci a gaba gare shi, da kuma qaunar samun rahamar Allah da gafararsa, tare da jin tsoron faxawa cikin azabar Allah da fushinsa, yana mai yin hisabi wa kansa, tare da jaddada tubansa lafiyayya, saboda wannan yini (na arafah) yini ne mai girma, cikin kuma taro babba, wanda Allah yake yin kyauta a cikinsa ga bayinsa, ya kuma yi alfahari da su ga mala'ikunsa, tare da yawaita 'yanta su a cikinsa daga wuta, kuma ba a tava ganin shexan a cikin wani yini da aka fi nisantar da shi daga rahamar Allah, yana kuma wanda ya fi qaranci da qanqanta fiye da yinin arafah, in banda yinin da aka yi yaqin badar a cikinsa, wannan kuma ya kan kasance ne saboda abinda shexan ya ke gani na kyautayin Allah ga bayinsa da kyautatawarsa a gare su, da yadda ya ke yawaita 'yanta su daga wuta a cikinsa yana mai gafarta musu.
Ya zo a cikin littafin sahihu Muslim, daga A'ishah (رضي الله عنها) lallai Annabi (r) ya ce:
«مَا مِنْ يَوْمٍ أَكْثَرَ مِنْ أَنْ يُعْتِقَ اللَّهُ فِيهِ عَبْدًا مِنَ النَّارِ مِنْ يَوْمِ عَرَفَةَ، وَإِنَّهُ لَيَدْنُو ثُمَّ يُبَاهِى بِهِمُ الْمَلاَئِكَةَ فَيَقُولُ: مَا أَرَادَ هَؤُلاَءِ؟».
Ma'ana: "Babu wani yini wanda Allah ya fi 'yanta bayi a cikinsa daga wuta fiye da yinin arafah, kuma lallai Allah yana kusantowa, sannan sai ya yi alfahari da su ga Mala'ikunsa, sai ya ce: Me waxannan su ka nufa?" ([4]).
Akan haka; ya dace ga musulmai su nuna wa Allah alherin da yake cikin zukatansu, su kuma wulaqanta maqiyinsa shexan, suna masu baqanta masa rai; ta hanyar yawaita ambaton Allah da kuma yawaita addu'oi, da tuba zuwa gare shi, tare da neman gafararsa daga dukkan zunubai.
Kuma mahajjata ba za su gushe ba a wannan matsaya suna masu shagaltuwa da zikiri da addu'a tare da qanqan da-kai, har zuwa lokacin da rana za ta faxi, idan kuma ta riga ta faxin to sai su tafi zuwa ga filin muzdalifah cikin nitsuwa da kwanciyar hankali, tare da yawaita yin talbiyyah, da kuma yin sauri in an samu sararin yin hakan, saboda Annabi (r) ya aikata hakan.
Kuma baya halatta a tafi a bar filin arafah gabanin faxuwar rana, saboda Annabi (r) ya tsaya ne, har zuwa faxuwarta, sannan kuma yace, na yi haka ne:
«لتأخُذُوا مَنَاسِكَكُمْ».
Ma'ana: "Don ku koyi aikin hajjinku"([5]).
Idan mahajjata suka sauka a filin muzdalifah sai su yi sallar magriba a wannan wurin; raka'oi uku, ishah kuma raka'oi biyu (wato: qasaru), suna masu aikata su a tare (jam'i), bayan yi musu kiran sallah guda xaya, da kuma iqamah biyu, za su yi haka daga zarar isowarsu, saboda haka Annabi (r) ya aikata, kuma wannan hukuncin haka ya ke ba banbanci; sawa'un isowar tasu ta kasance ne a lokacin sallar magriba, ko kuma a lokacin yin sallar ishah.




([1])  Muslim ya ruwaito shi, (lamba: 1218).
([2])  Tirmiziy ya ruwaito shi, (lamba: 3585), daga Amru xan Shu'aib, daga babansa daga kakansa.
([3])  Bukhariy ya ruwaito shi, (lamba: 299), da Muslim (lamba: 2137), daga Samurah xan Jundub (t).
([4])  Muslim ya ruwaito shi, (lamba: 1348).
([5]) Muslim ya ruwaito makamancinsa, (lamba: 1297), daga hadisin Jabir (t).

No comments:

Post a Comment

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...