2017/12/21

خطبة الحذيفي 4 ربيع الثاني 1439ه KAN AURE DA SHIKA A MUSULUNCE











HUDUBAR MASALLACIN ANNABI صلى الله عليه وسلم
JUMA'A, 4/RABIYUS SANIY/1439H
daidai da 22/DISEMBA/2017M




LIMAMI MAI HUXUBA
SHEIKH ALIYU BN ABDURRAHMAN ALHUZAIFIY





TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
Shehin Malami wato: Aliyu bn Abdurrahman Alhuzaifiy –Allah ya kiyaye shi- ya yi hudubar juma'a mai taken: AURE DA SHIKA A MUSULUNCI, Wanda kuma a cikinta ya tattauna, akan

بسم الله الرحمن الرحيم
HUDUBAR FARKO
Yabo ya tabbata ga AllahN da Ya halitta jinsin maza da mata, daga abinda kasa ke tsirarwa, da kuma cikin mutane, har da abinda mutane ba su sani ba.
Kuma Ubangiji Mabuwayi da daukaka ya yi umarni kan yin gyara da kawo gyara, ya kuma yi hani kan barna, a cikin fadinsa;
"Kuma ka kawo gyara, kada ka bi hanyar mabarnata" [A'araf: 142].
Sannan Allah (تبارك وتعالى) ya shar'anta shari'oi, domin maslahar bayi da amfaninsu, da tunkude barna da kuma dukkan ababen  da suke cutar da mutane da aljanu.
        Ina yabo ga Ubangijina, kuma ina gode masa, ina tuba zuwa gare shi, ina neman gafararSa,
Ina kuma shaidawa babu abin bautawa da gaskiya, sai Allah shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya, Mawadacin da bashi da bukatar talikai.
Kuma ina shaidawa lallai annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawansa ne manzonsa, Mai gaskiya, Amintacce,
Ya Allah! ka yi salati, da sallama da albarka ga bawanka kuma manzonka; Muhammadu, da iyalansa da sahabbansa gaba daya.

Bayan haka:
Ku bi Allah da takawa, a asirce da kuma a bayyane, saboda babu mutumin da ke samun rabo a cikin rayuwarsa, da bayan mutuwarsa, sai da takawa, kuma babu wanda zai tabe, ya yi hasara, sai ta hanyar bin son zuciya.

Ya ku mutane
Ku rika tuna mafarin halittarku (daga mutane biyu; Adamu da Hauwa'u), da yadda mazan cikinku da matanku suka yawaita, alhalin kun samu ne daga rai guda daya; Wanda Allah ya halitta masa matarsa daga jikinsa, Allah (سبحانه) ya ce: "Ya ku mutane, ku ji tsoron Ubangijinku wanda ya halitta ku daga rai guda, kuma ya halitta matarsa daga gare shi, kuma daga gare su, ya watsa maza dayawa, da mata" [Nisa'i: 1].
Kuma Allah Ta'alah ya ce: "Shi ne wanda ya halitta ku daga rai guda, kuma ya halitta masa matarsa daga gare shi, domin ya samu natsuwa da ita" [A'araf: 189].
        Sa'annan sai sunnar Allah da shari'arsa suka gudana, akan kulluwar namiji da mace ta hanyar kulla ko daura aure, irin na shari'a, domin mutane su iya gina gidan auratayya, kuma domin a amsa ga bukatar halitta; ta irin sha'awar da ke tsakanin mutane, da bin hanyar aure; ba ta hanyar zina ba, domin hanyar aure ita ce, ke haifar da kamewa, da albarka, da bunkasa, da tsarkaka, da arziki, da lafiyar zukata, da samun doriyar shekaru; ta hanyar zurriyar mutum nagari; wato salihai.
Ita kuma hanyar zina tana da dauda, ga janyo cutukan zuciya, da lalacewar namiji da mace, ga kuma irin kaskancin da sabo ke janyowa, da matsalolin rayuwa, da tafiyar da albarkar rayuwa, da samun matsaloli cikin 'ya'ya da jikoki, sannan sai azabar lahira, An ruwaito daga Abu-hurairah (رضي الله عنه) daga Annabi (صلى الله عليه وسلم) cikin abinda ya gani na abubuwan al'ajabi, a daren da aka yi masa isra'i da mi'iraji, Ya ce: "Sa'annan sai ya je ga wasu mutane, wadanda ake farfasa kayukansu da dutse, duk lokacin da aka fasa, sai kan ya koma kamar yadda ya kasance daga farko, kuma baza a dena aikata musu hakan ba. Sai ya ce: Su wanene wadannan Ya Jibrilu? Sai ya ce: Wadannan sune kansu ke yin nauyi kan halartar sallolin farilla.
Sa'annan sai ya je ga wasu mutane, wadanda aka sanya takardu ko fata ta gabansu, da kuma ta duburarsu, suna kai-komo, kamar yadda rakumi ko dabbobi ke kai-komo, kuma suna cin kayar rakuma (dari'in), da kuma cin itaciyar danyan wuta (zakkum), da tsakuwa ko duwatsun da aka dafa su da wuta. Sai ya ce: Su wanene wadannan Ya Jibrilu? Sai ya ce: Wadannan sune wadanda ba sa bayar da sadakar dukiyarsu (zakkah), kuma Allah bai zalunce su da komai ba.
Sa'annan sai ya je ga mutanen da a gaba gare su akwai dafaffen naman da ke cikin tukunya, da kuma wani naman danye a cikin wata tukunyar mai dauda, amma sai gashi suna cin wannan danyen mai dauda, suna barin nunannen mai tsafta, Sai ya ce: Su wanene wadannan Ya Jibrilu? Sai ya ce: Wannan mutum ne daga cikin al'ummarka, zai kasance yana da mace ta halal, mai tsafta, sai ya je wurin wata mace mai dauda, sai ya kwana a wurinta, har safiya. Da kuma matar da za ta tashi daga wurin mijinta na halal mai tsafta, sai ta je wurin wani namji mai dauda; ta kwana da shi, har safiya". Ibnu-Jarir ya ruwaito shi a cikin tafsirinsa.
Kuma ya zo cikin hadisin Sa'ad bn Sinan Alkhudriy (رضي الله عنه) daga Annabi (صلى الله عليه وسلم) akan isra'i da mi'iraji, ya ce: "Sa'annan sai na yi gaba kadan, sai ga ni a wurin wasu kwanukan da suke dauke da nama a cikinsu a yayyanke, amma babu wanda ke kusantarsu, sai ga ni a wurin wasu kwanukan da suke dauke da naman da yake doyi, a wurin kuma akwai mutanen da suke cin wannan naman. Sai na ce: Ya Jibrilu, su wanene wadannan? Ya ce: Wadannan daga cikin al'ummarka, suna barin halaliyarsu, sai su je ga haram. Ya ce: Sannan sai ya matsa gaba kadan, sai ga ni wurin wasu mutanen da cikkinsu kamar gidaje, duk lokacin da dayansu ya yunkura don ya tashi sai ya fadi, yana cewa: Ya Ubangijina, kada ka tashi kiyama. Sai ya ce: kuma su suna kan hanya irin ta iyalan fir'auna. Ya ce: Sai hanyar ta zo, ta rika tattaka su, Sai ya ce: Wadannan a cikin al'ummarka sune masu cin riba, "Wadanda suke cin riba baza su tashi ba, sai kamar wanda shedan ke dimautarwa daga shafa ke tashi" Baihakiy ya ruwaito shi a cikin littafin Dala'ilun nubuwwati.

Gidan aure mafaka ce da ke bada kulawa ga zurriya, kuma take tausaya musu, take damuwa da su, take ilmantar da su.
Kuma uwa da uba sune ke shirya al'umma ('ya'ya da jikoki) domin su iya daukar nauyace-nauyacen rayuwa, da amfanar da daukacin al'umma, da bunkasa yara cikin kowane sha'ani, kuma sune suke fadakar da su zuwa ga riko da kowace dabi'a mai kyau, su kuma yi hani kan aiki da kowace dabi'a abar aibantawa, kuma su rika bada tarbiyya akan aikin kwarai, domin neman dacewa da gidan lahira, da kuma rayuwa ta har abada, kuma sai karamin yaro ya yi koyi da abinda yake gani a gida, sai kuma ya tasirantu da abinda ya ke gani, kuma ya ke ji, tun da bashi da ikon karanta tarihi, domin daukar izina daga cikinsa, da kuma abin koyi.

Shi kuma daura aure ko kulla shi, alkawari ne mai girma, kuma igiya ce mai karfi, kuma zumuncin sadarwa mai tsananin muhimmanci, Allah (تعالى) ya ce: "Kuma idan kun yi nufin musanya mace, a gurbin wata macen, kuma kun baiwa dayansu tarin dukiya (kindari), to kada ku karbi wani abu daga cikinsa, Shin za ku karbe shi da karya da zunubi bayyananne? * Kuma yaya za ku karbe shi, alhalin, sashenku ya sadu da sashe, kuma mata sun riki alkawari mai kauri daga gare ku" [Nisa'i:20-21].
Maluman tafsiri suka fassara alkawari mai kauri da cewa, shine: Daura aure.

Kuma daura aure, yana kunsar maslahohi da amfani ga miji da mata, da wasu amfani da maslahohin na 'ya'ya, da maslahohi da amfani ga makusantan ma'auratan biyu, da kuma wasu amfani da maslahohin ga daukacin al'umma, da  wasu maslahohin na duniya da lahira, wadanda ba za a iya kididdige wadannan amfanonin ba.

Shi kuma warware wannan alkawarin, da lalata wannan kullin, da tsinke igiyar auratayya, ta hanyar SHIKA, yana rurrushe wadancan maslahohin da amfanonin gaba dayansu. Sai miji ya auka cikin fitintinun da za su cutar da shi ga addininsa da duniyarsa da lafiyarsa.
Kuma itama mace, idan aka sake ta, sai ta auka cikin fitintinun da suka fi tsanani akan wanda mijin ke aukawa cikinsu, kuma wanda aka sake ba za ta samu ikon mayar da rayuwarta kamar yadda ta kasance ba, kuma sai ta rayu cikin nadama, musamman a wannan zamanin wanda a cikinsa mazajen da za su iya dacewa da halinta suka yi karanci, sai 'ya'yansu su watse, su kuma fiskanci rayuwa mai matukar tsanani, wacce ta banbanta da wanda suka yi alhalin suna karkashin inuwa ko kulawar iyaye guda biyu (uwa da uba) a hade, sai kuma su rasa dukkan dadin da zai sanya rayuwarsu cikin walwala, sai su fiskanci lalacewar halayya da nau'ukansa mabanbanta, da kuma cutuka iri-iri, sai itama al'umma gaba dayanta, ta cutu, da matsaloli masu cutarwa, wanda su ke kasancewa bayan aukuwar shika, sai ka ga, yanke zumunta yana yawaita.
Kuma duk yadda aka kai makura wajen kididdige matsalolin da suke cikin shikar aure, to lamarin ya fi haka.
Kuma, domin ka san barnar da shika ke haifarwa, da yawaitar matsalolinta, kebantattu da masu gamewa, sai ka yi tunani cikin hadisin Jabir (رضي الله عنه) daga Annabi (صلى الله عليه وسلم), lallai ya ce: "Lallai Iblisu ya kan dora al'arshinsa ko gadon mulki akan ruwa (teku), sa'annan ya tura 'yan farautarsa, kuma wanda zai fi su kusancin matsayi da Iblisu shine wanda yafi tsananin fitina; Sai daya daga cikinsu ya zo, ya ce: Na aikata kaza, da kaza, Sai ya ce: Ba ka aikata komai ba. Sa'annan sai daya daga cikinsu ya zo ya ce; Ban bar wane ba, har sai da na raba tsakaninsa da tsakanin matarsa; Sai Iblisu ya kusantar da shi, yana cewa: Na'am, Kai ne goga, Sa'annan sai ya rungume shi", Muslim ya ruwaito shi.

Kuma lallai wasu mutane, sun yi sako-sako da batun shika, sai suka dauki lamarinsa da sauki, sai su ka auka cikin lamura masu hatsari, da sharrace-sharrace masu tarin yawa, sannan su kan aukar da wasunsu cikin abinda suka auka a cikinsu.
Hakika shika saboda sabuba masu rauni, ya yawaita a wannan zamanin, ko saboda dalilai marasa kan-gado.
Kuma SABBUBAN SHIKA A WANNAN ZAMANIN suna da yawa,
Yana daga MAFI GIRMANSU: JAHILTAR HUKUNCE-HUKUNCEN SHIKAN, a cikin shari'a, da rashin aiki da Kur'ani da sunnah. Saboda shari'ar musulunci ta kewaye kullin aure, da dukkan abinda zai bashi kariya da kula, kuma ta kare aure da muhimmiyar katanga, domin bashi kariya; kuma domin kada ya tsattsage, ya rushe, ya girgiza; a lokacin kadawar guguwar son zuciya.
Kuma domin kasancewar sababin shika ka iya kasancewa daga miji, ko daga matar, ko daga miji da matar, ko daga wasu daga cikin makusantansu; Sai shari'a ta magance kowane irin yanayin da ka iya zama sababin shika;
Sai Allah a cikin littafinsa ya umarci miji, da ya girmama lamarin aure, Allah (تعالى) ya ce: "Kuma kada ku rike mata da cutarwa; har ku kekare iyaka, kuma duk wanda ya aikata hakan, to ya zalunci kansa, kuma kada ku riki ayoyin Allah da izgili" [Bakara: 231].
Kuma Allah ya ce: "Kuma su mata, suna da kwatankwacin abinda ke kansu (na hakkoki) da kyautatawa, Kuma su maza suna da wata daraja akan mata" [Bakara: 228].
        Maluman tafsiri suka ce:
Mace akan mijinta, tana da hakkoki, misalin hakkokin mijin da ke kan matarsa, wajen kyautata zamantakewa, Sai kuma namiji ya samu fifiko akan mace, ta fiskar kasantuwarsa mai tsayuwa da lamarinta, .
Don haka wajibi ne, akan namiji yayi zamantakewa da matarsa cikin abinda aka sani da kuma kyautatawa, Idan kuma ya kita, to sai ya dau hakuri, la'alla yanayin ya canzu, izuwa ga wanda yafi kyau, ko la'alla a azurta shi da 'ya'ya salihai tare da ita, sannan a bashi ladan hakurinsa, Allah (تعالى) ya ce: "Kuma ku yi zamantakewa da su da kyautatawa, domin idan kun ki su, to, tana yiwuwa ku ki abu, sai Allah ya sanya alkhairi mai yawa a cikinsa" [Nisa'i: 19].
        Kuma wajibi ne ga miji da matarsa, su rika gyara lamuran da suke janyo sabani, tun suna farko-farkonsu; domin kada kafar sabanin ta fadada.
        Kuma wajibi ne ga miji da mace; kowannensu ya san dan'uwansa; sai kowanne ya rika aikata abinda zai fi yardar da sahibinsa, Ya kuma rika nisantar abinda dayan baya so, Wannan kuma abu ne mai sauki, da ba a boye ya ke ba.
       
        YANA DAGA CIKIN SABBUBAN WANZUWAR AURE: Kokarin yin sulhu a tsakanin ma'auratan, daga ma'abuta alkhairi, masu sulhuntawa, da kawo gyara, domin kowanne ya iya samun hakkokinsa na wajibi, wanda ke kan sahibinsa, Allah (تعالى) ya ce: "Kuma idan ku ka ji tsoron sabani a tsakaninsu, sai ku tayar da mai hukunci daga cikin iyalansa, da mai hukunci daga iyalanta, idan sun nufi sulhu a tsakaninsu, to lallai Allah zai daidaita tsakaninsu, Lallai ne Allah ya kasance Masani Mai bada labari" [Nisa'i: 35].

        KUMA YANA DAGA SABBUBAN DAWWAMAR AURE DA JIN DADINSA: Hakuri da yin rangwame, domin dacin da ke cikin hakuri, dan kadan, zaki ne na tsawon zamani ke biyo bayansa, Kuma ba wani abinda ake fiskantar ababen ki da shi, wanda ya kai hakuri girma, Allah (تعالى) ya ce: "Kawai, masu hakuri ana cika ladansu, ba tare da lissafi ba" [Zumar: 10].
        Rangwame da yin afuwa, suna kawata rayuwa, kuma suna sanya ma rayuwa walwala da farin ciki da kyau. Kuma da shi ake warkar da kurjin da zamantakewa ta haifar. Kuma, Yafiya da yin afuwa dole ne a rayuwa, musamman kuma tsakanin ma'aurata biyu.
Kuma idan ya kasance cikin lamura ne na karin kwalliya (ba wajibi ba), Ko kuma cikin lamuran da za a iya jinkirta su, to lallai yin rangwame a irin wannan, shine mafi alheri ga ma'aurata. Musamman kuma a irin wannan zamanin, wanda kokarin samar da bukatun rayuwa, ya wahalar da yawa-yawan mazaje, tare da cewa, wasu ababen ba na lalura ko dole ba ne.
Kuma lallai neman bada dukkan hakkoki, da rashin rangwantawa, ko yafe wasu hakkokin, yana gadar da guje wa juna da kiyayya a tsakanin ma'aurata. Alhalin shi kuma aure ruhinsa shine, taimakakkeniya, da jin-kan juna, Allah (تعالى) ya ce: "Ya ku wadanda suka yi imani lallai ne wasu daga matanku da 'ya'yanku makiya ne a gare ku, sai ku kiyaye su, kuma idan kuka yafe kuma kuka kau da kai, kuma kuka gafarta, to lallai Allah Mai gafara ne Mai jin kai", [Tagabun: 14].
Gabar da ake nufi a wannan ayar ita ce, sanyaya guiwar miji ko uba kan aikata alkhairi, ko kuma rashin taimakonsa, ko kuma hana shi aikata aikhairin.
Kuma Allah (تعالى) ya ce: "Ka riki abinda ya saukaka, kuma ka yi umarni da alheri, kuma ka kau da kai daga jahilai" [A'araf: 199].

KUMA YANA DAGA SABBUBAN DAWWAMAR AURE: MIJI ya yi ta kokarin gyara abinda ya karkace na halin matarsa, da abinda shari'a ta halatta, kuma ta yi izini, Allah (تعالى) ya ce: "Su salihan mata masu da'a ne, masu tsarewa ga gaibi saboda abinda Allah ya tsare. Su kuma wadanda ku ke tsoron bijirewarsu, to, ku yi musu gargadi, kuma ku kaurace musu a wuraren kwanciya, kuma ku doke su, Idan kuma suka muku da'a, to kada ku nemi wata hanya akansu" [Nisa'i: 34].

Kuma wajibi ne akan alkalai su rika yin sulhi tsakanin ma'aurata biyu, cikin abinda ake kaiwa gare su na kararraki, har a samu ittifaki, a kawar da shika.

Shi kuma HAKKIN MACE AKAN MIJINTA shi ne ya yi zamantakewa da ita da kyautatawa, ya kuma bata gidan da ya yi daidai da irinta, tare da ciyarwa da tufatarwa, da bayar da alkhairi, da kamewa ga barin cutar da ita.

Kuma lallai SABABIN SHIKA YANA IYA KASANCEWA DAGA MATAR NE, saboda kaushin harshenta, ko munin halinta, da jahilcinta, Don haka, wajibi ne akan mace ta rika gyara halinta, tana mai biyayya ga mijinta, ta yi bakin kokarinta wajen tarbiyyar 'ya'yanta da ingantacciyar tarbiyya, An ruwaito daga Abdurrahman bn Auf (رضي الله عنه) daga Annabi (صلى الله عليه وسلم), ya ce: "Idan mace ta yi sallolinta biyar, ta yi azuminta na wata, ta kiyaye farjinta, ta yi biyayya ga mijinta, Sai ace mata: Ki shiga Aljannah, daga dukkar kofar da ki ka so", Ahmad ya ruwaito shi, kuma hadisi ne hasan.

Kuma wajibi ne ga mace ta rika hidima ga mijinta, da kyautatawa, tana mai koyi da sahabbai mata –رضي الله عنهن-.
Kuma abu ne mai kyan gaske ta rika yin tarayya da mijinta cikin farin cikinsa da bacin ransa, kuma ta kasance mai taimakonsa wajen biyayya ga Allah Ta'alah.

KUMA YANA DAGA SABBUBAN SAMUWAR SHIKA: Shisshigin wani daga dangin miji ko mata, ko kuma danginsu gaba daya, Sai su ji tsoron Allah, kuma su fadi magata ta daidai. Kuma ya zo cikin hadisi, cewa: "Allah ya la'anci mutumin da ya bata matar wani a gare shi, ko kuma ya bata mijin ga matarsa".

Kuma wajibi ga MACE TA TSAYU WAJEN BADA HAKKIN MAKUSANTAN MIJINTA, musamman kuma iyayensa biyu.
Kuma shima mijin WAJIBI NE YA TSAYU WAJEN BAYAR DA HAKKIN MAKUSANTAN MATARSA; saboda sakaci kan hakkin makusantan ma'aurata, sau dayawa ya kan zama sababin shikan aure.

KUMA YANA DAGA SABBUBAN SHIKA: Bibiyar fina-finan da su ke rushe dabi'a, ko shafukan yanan gizo-gizo (internet) na haram, wadanda suke yada barna.

KUMA YANA DAGA SABBUBAN SHIKA: Fitan mace daga gida ba tare da samun izinin mijinta ba , kuma baya halatta a gare ta, ta fita ba tare da izininsa ba, domin miji shine ke da ma'aunin auna lamura.

Kuma idan SABBUBAN ZAMAN AURE SUKA GAGARA To lallai Allah ya halatta yin shika, kuma ya zo cikin hadisi cewa: "Halal din da Allah ya fi kinsa, shine shika".

Sai miji ya yi shika irin na shari'a, bayan tsanaki da bi-sannu-sannu, kamar yadda Allah ya yi umarni a cikin fadinsa: "Ya kai wannan Annabin idan za ku saki mata, sai ku sake su ga iddarsu, kuma ku kididdige iddar" [Dalak: 1].
Maluman tafsiri suka ce:
Sai ya sake ta a cikin tsarkin da bai sadu da ita a cikinsa ba, shika daya, Idan ya so, sai ya mata kome a cikin wannan iddar. Idan kuma ya so, sai ya barta har ta gama iddarta, sai ta fita daga mulkinsa.
Kuma lallai shika ta irin wannan hanyar tana bude kofar fatan yin kome, don wanzar da auren, ko a sake sabon aure, idan har ta yi tsarki, bayan idda.

Sai ka yi dubi, ga yadda aka karfafa lamarin aure, da yadda shari'ar gaskiya ta kiyaye shi. Kuma ka yi dubi kan sakacin mutanen wannan zamanin kan lamarin shika, da abinda shikan ke janyowa; na kayan bacin rai.
Allah (تعالى) yana cewa: "Ya ku wadanda suka yi imani, kada ku bi, hanyoyin shedan, domin duk wanda ya bi hanyoyin shedan, to lallai shi yana umarni ne da alfasha, da kuma munkari", [Nur: 21].

Allah ya yi mini albarka NI da KU, cikin alqur'ani mai girma, ya kuma amfanar da NI da KU da abinda ke cikinsa na ayoyi, da tunatarwa mai hikima,      Na faxi abinda ku ka ji, kuma ina neman gafarar Allah mai girma ga Ni da KU da kuma sauran Musulmai daga kowani zunubi, Ku nemi gafararSa,    lallai shi Mai gafara ne Mai rahama.
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,

HUXUBA TA BIYU
        Yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai, Mai rahama Mai jin-kai, ya shar'anta hukunce-hukunce da iliminsa da hikimarsa da kuma rahamarsa.
Tsarki ya tabbata a gare shi; abin bauta Mai girma.
Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya, Masani Mai hikima.
Kuma ina shaidawa lallai annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawanka ne kuma manzonka,

Ya Allah ka kara salati da sallama da albarka ga bawanka kuma manzonka Muhammadu, da iyalansa, da sahabbansa, masu riko da shari'arsa mikakkiya.

Bayan haka … !!
Ku ji tsoron Allah, iyakar tsoronsa, kuma ku yi riko a musulunci da igiya mai karfi.

Ya ku Bayin Allah … !!
Allah yana cewa:  "Kuma ku taimaki juna akan biyayya da takawar Allah, kada ku taimaki juna akan sabo da ketare iyaka, kuma ku ji tsoron Allah, lallai ne Allah Mai tsananin ukuba ne" [Ma'ida: 2],

Ya ku Musulmai,
Shika ya zama wani abinda ke gudana akan harasan wasu samarin ba tare da tsare ko kula da hakkokin 'ya'yansu, ko wani makusancinsu ba, ko kuma lura da wani ba,
Kuma hakan yana aukuwa, ta hanyar maimaita shi, a cikin zamani masu nisa da juna, ko maimaita fadinsa a cikin majalisa daya, sai kuma ya tafi yana ta neman fatawowi, ko ya ce, zai yi wayo, wani lokacin hanyoyi su kan toshe masa, sai ya yi ta nadamar da ba za ta masa amfani ba, Alhalin Allah kuma yana cewa: "Duk wanda ya ji tsoron Allah, to zai sanya masa mafita * kuma ya azurta shi, ta yadda baya tsammani" [Dalak: 2-3].
Kuma duk wanda ya ji tsoron Allah, cikin lamarin shikansa, ta fiskar da shari'a ta yarda, sai Allah ya sanya masa mafita.
Kuma duk wanda ya dauki aure da girma, bai yi sako-sako da shi ba, sai Allah ya sanya masa albarka a cikin aurensa, kuma ya samu kyakkayawar natija.

Kuma wasu daga cikin na'ukan shika kebantattu, yin shika a cikin wadannan halayen ya kan kasance laifi ne (sabo), kamar yadda Annabi (صلى الله عليه وسلم) ya ce wa Abu-Ayyub: "Lallai sake Ummu-Ayyub, laifi ne".

Ya ku bayin Allah!
"Lallai ne, Allah da Mala'ikunsa suna yin salati ga wannan annabin, Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi salati a gare shi, da sallama ta aminci" [Ahzab: 56].
 ……………………………
,,,          ,,,          ,,,


2017/12/08

Hudubar Dr Buaijan 20 Rabiul Awwal 1439 daidai 8 Disemba 2017











HUDUBAR MASALLACIN ANNABI صلى الله عليه وسلم
JUMA'A, 20/RABI'UL AWWAL/1439H
daidai da 8/DISAMBA/ 2017M




LIMAMI MAI HUXUBA
SHEIKH ABDULLAHI BN ABDURRAHMAN ALBU'AIJAN





TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
SHIRI GA AZUMIN RAMADHANA
Shehin Malami wato: Abdullahi bn Abdurrahman Albu'aijan –Allah ya kiyaye shi- ya yi hudubar juma'a mai taken: , Wanda kuma a cikinta ya tattauna, akan

بسم الله الرحمن الرحيم
HUDUBAR FARKO
Yabo ya tabbata ga Allah; wanda zamani ke juyawa da umarninSa, kuma lokatai ke riskar juna da izininSa, "Yana shigar da dare akan yini, kuma yana shigar da yini akan dare" [zumar: 5], Ya sanya rana ta zama babban haske mai zafi, wata kuma mai haske, kuma ya kaddara shi manziloli, domin ku san kidayar shekaru da lissafi [Yunus: 5].
Ina yin yabo ga Ubangijina, saboda shine ma'abucin yabo da girma, kuma ina yin godiya a gare shi akan ni'imominSa da basu kididdiguwa ko kirguwa.
Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya, sai Allah; shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya, cikin sha'aninSa,
kuma ina shaidawa lallai annabi Muhammadu bawanSa ne manzonSa, mai kira ga samun yardarSa, Wanda ya turo shi da shiriya da kuma addinin gaskiya, domin ya daukaka shi akan addinai gaba daya, koda mushirkai sun ki [Tauba: 33].

Allah ka yi karin salati a gare shi, da iyalansa da sahabbansa, da wanda ya shiryu da shiriyarsa, ya kuma bi sunnarsa, har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka:
Lallai mafi gaskiyar zance shine littafin Allah, kuma mafi karfin igiya ita ce, Kalmar takawa (ta LA ILAHA ILLAL LAHU), Kuma mafi alherin addinai shine addinin annabi Ibrahima, kuma mafi kyawun kissosi shine na cikin Kur'ani, kuma mafificiyar shiriya ita ce shiriyar Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم), kuma mafiya sharrin lamura sune kagaggu daga cikinsu, kuma kowace bidi'a bata ce.
Ina yin wasici a gare ku, da ni; kaina, da tsoron Allah Mabuwayi da daukaka a asirce da kuma a bayyane, saboda takawa ita ce tsira a duniya mai karewa, kuma dalilin samun babban rabo a lahira mai wanzuwa, "Ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah, kuma ku fadi magana madaidaiciya * Zai kyautata muku ayyukanku, kuma ya gafarta muku zunubanku, kuma wanda ya yi da'a ga Allah da ManzonSa, to lallai ya rabauta da babban rabo mai girma" [Ahzab: 70-71].
Ya ku bayin Allah
A wasu yinin, mutane kan nemi kariya daga matsanancin zafin tsakiyar rana, ko kunar lokacin zafi. A wani yinin kuma, sai mutane su shirya domin tunkarar funturun sanyi, sai kuma su nemi wanduna da kayan sanyi. To, lallai cikin hakan akwai babban wa'azin jan-kunne ga ma'abuta basirori; domin tsananin sanyi, da kuma tsananin zafi, numfashi ne guda biyu, na Jahannama; Hadisi ya zo daga Abu-hurairah –رضي الله عنه-, a lokacin da ya ce: "Manzon Allah –صلى الله عليه وسلم- ya ce: Idan zafi ya tsananta to, ku sanyaya sallah; domin tsananin zafi yana daga numfashin Jahannama, kuma wutar ta kai kukanta zuwa ga Ubangijinta; a inda ta ce: Ya Ubangijina, lallai sashena ya cinye sashe, Sai ya mata izinin ta rika numfashi guda biyu; numfashi daya a lokacin sanyi, numfashi dayan kuma a lokacin zafi. Don haka, Duk abinda kuka samu na sanyin jaura, to yana daga numfashin jahannama, kuma duk abinda kuka samu na yanayin zafi ko zazzafar iska, to daga numfashin Jahannama ne". Bukhariy da Muslim.
To, Menene zatonku –Ya ku bayin Allah- dangane da wutar jahannama?
Lallai ita ce wutar Allah wanda ake furawa, * wanda take lekawa akan zukata" [Humaza: 6-7]. "Lallai ne ita tana yin jifa da tartsatsi kamar benayi, * kamar dai su rakummai ne fatsatse" [Mursalat: 32], "Bata ragewa kuma bata bari * mai nacewa ce ga jiki da kuna * akanta akwai masu tsaro guda goma sha tara" [Mudassir: 28-30], "A aha, lallai ne fa ita ce wutar laza * mai twale fatar goshi * tana kiran wanda ya juya baya (daga addini) kuma ya kauda kai * ya tara dukiya, kuma ya kiyaye ta" [Ma'arij: 15-18], kuma lallai ita ce "wutar hawuya * kuma me ya sanar da kai mecece ita? Wata wuta ce mai zafi" [Alkari'ah: 9-11].
An kunna ta, aka iza, na tsawon shekaru dubu, har ta zama kalar ja, sa'annan aka iza ta, na tsawon shekaru dubu, har ta koma fari, sa'annan aka sake iza ta na tsawon shekaru dubu har ta zama baki, don haka, ita baka ce, kirin. Wacce tartsatsinta baya yin haske, baki-n wutar kuma, baya mutuwa;
"Sai ku ji tsoron wutar da makamacinta sune mutane da duwatsu" [Tahrim: 6],
Hadisi ya zo daga Abu-hurairah, lallai Annabi –صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Wutarku wanda 'dan-adam ke furawa, bangare ce guda, daga bangarori saba'in na zafin wutar Jahannama", Sai suka ce: Idan ta kasance kamar ta duniya ita ma ta wadatar? Ya ma'aikin Allah! Sai ya ce: "Lallai an fifita wutar lahira akan ta duniya, da bangare sittin da tara, dukkansu zafinsu kamar nata". Allah ya tsare mu da ku, daga aukawa wuta.

Ya ku taron musulmai
Lallai sunnonin rayuwa suna gudana ne cikin wani tsari mai ban kayatarwa, da hukuncin Allah da lamarinsa abin sallamawa, kuma Allah ya kan ji-kan wanda ya nufa da wadannan sunnonin sai su amfanar da shi. Kuma ya kan yi ibtila'i ga wanda ya so, da su, sai su cutar da shi; saboda haka, an hore wadannan sunnonin da nufin Allah, kuma basu da nufin zartarwa ko ikon juya komai, "Wannan shine Allah Ubangijinku, mulki nasa ne, su kuma wadannan da ku ke roko baicinsa, basu mallakar koda fatar bayan dabino" [Fadir: 13].

Hakika Allah ya taimaki annabi Nuhu, da ruwan Dufana, sai ya halakar da mutanensa ta hanyar nitsarwa a cikin ruwa, Sai kuma ya tsamar da shi, da wadannan da suka yi imani da shi.

Kuma Allah ya bada nasara ga annabi Musa, da teku, ya kuma nitsar da fir'auna a cikinsa, da wadanda suke tare da shi.

Kuma ya taimaki annabi Hudu, sai ya halakar da mutanensa da iska kaikasasshiya, wanda bata barin abinda ta bi ta kansa face, ta sanya shi kamar rududdugagen kashi.

Kuma ya taimaki annabi Salihu, sai ya halakar da mutanensa, da tsawa, alhalin suna gani, kuma basu samu damar tsayawa ba, kuma basu kasance wadanda za a agaza musu ba.

"Kuma kowannensu mun kama shi da laifinsa, kuma daga cikinsu akwai wanda muka aika iskar tsakuwa akansa, kuma daga cikinsu akwai wanda tsawa ta kama, kuma daga cikinsu akwai wanda muka birkice kasa da shi, kuma daga cikinsu akwai wanda muka nitsar. Kuma baya yiwuwa ga Allah ya zalunce su, amma sun kasance kansu suke zalunta" [Ankabut: 40].
Don haka, ababen da suke aukuwa a cikin duniya, dukkansu a hannun Allah suke, kuma karkashin nufin Allah, bashi da abokin tarayya, a cikin hakan.

A UZU BILLAHI MINAS-SHAIDANIR RAJIM:
"Kuma na Allah ne, mulkin sammai da kasa, kuma zuwa ga Allah makoma take" [Nur: 42].

Allah ya yi albarka ga ku, da ni cikin alkur'ani mai girma, ya kuma mafanar da ni da ku da abinda ke cikinsa na ayoyi da tunatarwa mai hikima, Ina fadan abinda kuke ji, kuma, …

,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,

HUDUBA TA BIYU
        Yabo ya tabbata ga Allah, wanda ya halicci sammai da kasa, kuma ya sanya duffai da haske [An'am: 1], mai juya yinnai da watanni, kuma mai karar da shekaru da zamannai, ina yin yabo a gare shi a dukkan lamari.
Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya.
Kuma ina shaidawa lallai annabi Muhammadu bawanSa ne manzonSa
Allah ya kara salati a gare shi, da iyalansa da sahabbansa.

Ya ku bayin Allah !! …
Lallai sanyin lokacin funturu yana dauke da wahalar da ta sanya hukunce-hukuncen shari'a basu gafala da shi ba, Sai mai shari'a ya yi rangwame kan ayi shafa akan safa (huffi) domin dauke wahala, a kuma yi taimama idan za a cutu, kamar yadda aka shar'anta yin sallar rokon ruwa, idan aka samu fari a lokacinsa, da kuma yin addu'ar neman sama ta washe (ko tsayawar ruwa), a yayin bukatar hakan; saboda wahala tana janyo sauki, kuma Ubangiji bai sanya muku wani kunci a cikin addini ba. Wannan kuma an shar'anta su ne, ba wai domin kaiwa makura wajen walwala ne ko hutu ba, A'a, saboda Allah ya tayar da ManzonSa da shiriya, da addinin gaskiya, domin ya daukake shi akan addinai gaba daya, koda mushirkai sun ki. Kuma sai ya zabar masa da wannan yankin tsakiya na duniya, wanda ya hada matsanancin zafin kudancin duniya, da kuma funturun sanyin da ke arewacinta, sai ya cancantar da shi (da sauran mazauna wannan yankin) zamowa matsakaitan mutane tsaka-tsaki, wajen iya jure wa dabi'ar yanayi; ta fiskar zafinsa da sanyi, har su iya jure daukar sakon manzanci zuwa ga duniya gaba daya;
Sai Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya kasance yana dora sahabbansa akan jure wa wahalhalun tsananin zafi da sanyi, a cikin halin yunwa da kishi, yana mai karfafa musu cewa, gwargwadon wahala shine gwargwadon iya cimma buri, kuma ba a iya riskar daukaka ko samunta, sai bayan an ci wahala, kuma aljanna an kewaye ta ne da ababen da rai ke ki, kamar yadda aka kewaye wuta da sha'awoyi, kuma ni'ima ba a riskarta da ni'ima.
Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya fita zuwa ga yakin Ahzab, domin ya hadu da makiyansa, alhalin mayaka dubu goma sun yi tarun-tarume akansa, Sai Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya fita shi da sahabbansa a lokacin matsanancin sanyi, da kuma jure wahalwalu da bacin rai da gajiya, tare da hakurin kishi da yunwa, Huzaifah (رضي الله عنه) yana cewa: "Da dai, wani dare bai taba zuwa mana, wanda yafi tsananin dufu, ko yafi tsananin sanyi, ko yafi tsananin tasowar iska, kamar wannan daren ba, saboda sautin iskar da ke tashi a cikin daren kamar misalin sautin tsawa ne, ga matsanancin dufun da ya kai dayanmu baya iya ganin yatsarsa".

Kuma Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya fita yakin Tabuka ne cikin mayaka dubu talatin, a yanayin bugun iskar zafi mai tsanani, har munafikai suke fadin maganganun sace guiwa, suna cewa: "Kada ku fita zuwa ga yaki a cikin zafi" [Tauba: 81]. Sai Allah ya mayar musu da martini: "Kace wutar jahannama, tafi tsananin zafi, da sun kasance suna da sani" [Tauba: 81].
Umar (رضي الله عنه) ya ce: "Mun fita zuwa ga yakin Tabuka ne a lokacin matsanancin zafi, sai muka yada zango a wani masaukin da kishi ya kama mu, har sai da muka yi zaton wuyoyinmu zasu yayyanke, kuma har sai da ya zama, mutum yana soke rakuminsa, sai ya matse abinda ya saura a cikin tunbinsa don ya sha, ya kuma sanya abinda ya saura akan hantarsa".
        To, haka Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya ilmantar da sahabbai kan sadaukarwa ga wannan addinin, da kuma yin jihadi fi sabilil Lahi, a cikin sauki ko tsanani da cuta da lokacin yaki, ya kuma koya musu rayuwar wahala, da juriya, da yin hakurin aiwatar da aikin da'a.

        Ya ku bayin Allah
Lallai Allah ya mana baiwar ni'imomin da ba a iya kididdige su, kuma ya kwararo mana ni'imominSa na zahiri da na boye, saboda karamcinsa da kyautarSa da falalarSa. Kuma hakika ya halicce mu domin yin bauta a gare shi; don haka wajibi ne akanmu mu forar da kayukanmu don yin biyayya a gare shi, a cikin wahala da sauki, a lokacin nashadi ko ki, a halin lafiya da walwala, ko cuta.
Kuma wajibi ne mu yi amfani da ni'imomin Allah wajen yin biyayya a gare shi, mu yi kwadayin su zama taimako a gare mu, wajen aikata ababen da za su yardar da Shi, kuma sababin shiga aljannoninSa.
Muna kuma neman tsarin kan aiki da ni'imomin da ya yi akanmu, wajen saba masa, ko su kasance sababin fushinSa da azabarSa.

Ya ku bayin Allah
Kyautayi ga halittu yana tunkude mummunan kaddara, kuma mafi girman abinda ake tunkude musibobi da bala'i da su, kuma yake janyo albarka da bunkasar dukiya, shine: Tallafawa fakirai, musamman a lokacin shigan funturu, saboda akwai daga cikin fakirai wanda sanyi ke addabarsa ba tare da tufa ba, daga cikinsu kuma akwai wanda yunwa ke kayar da shi, ba tare da yana da riyal daya ko dinari ba, daga cikinsu kuma akwai wanda ruwan kasa da na sama ke malale musu mahallai, daga cikinsu akwai gajiyayyu da marayu da zawarawa da tsofaffi masu yawan shekaru, kuma daga cikinsu akwai makusanci ta fiskar dangantaka, da bako, da makwabci.
Sai ku yi laluben 'yan'uwanku mabukata, kuna masu farawa da danginku, da ma'abuta zumuncinku, sa'annan sai makwabtanku da garinku, sa'annan sai wanda suka fi kusa da ku; bi da bi, kuma kada mutum ya raina kyakkawan abu, duk karancinsa.
Ku rika yaye musu bakin ciki, ku taimaki wanda aka zalunta, ku tallafawa mutumin da aka masa rauni, "kuma ku ji toron Allah, wa la alla sai a yi muku rahama".

Ya ku taron musulmai
Lallai bada kariya ga kasa, ko garurrukan musulunci, kare asalin musuluncin ne, da abinda musulmai suka mallaka, da mutuncinsu da ababen mallakarsu. Kuma musulmai gaba dayansu gini ne guda daya, kuma al'umma daya, kuma gangan jiki daya, ta yadda idan wata gaba ta koka, sai sauran jikin ya amsa, ta hanyar zazzabi da kasa yin barci.
Kuma duk wani ta'addancin da zai taba tubali daya daga ginin musulmai, da garurrukansu, to lallai ta'addanci ne ga alfarmar dukkan musulmai, To, yaya kuma idan ta'addancin ya kasance ga Kudus ne? Yaya idan ta'addancin ya kasance ga kudus ne? wurin saukar wahayi, wurin da aka tayar da Annabawa da Manzanni, kuma alkiblan annabawa wanda musulmai suka fiskance ta da sallolinsu, a wani zamani na tarihi, wurin da aka yi Isra'i da Annabi (صلى الله عليه وسلم), kuma mihirabinsa wanda a cikinsa ya limanci dukkan annabawa (عليهم الصلاة والسلام) a salla.
"Tsarki ya tabbata ga wanda ya yi isra'i da bawansa, cikin dare, daga Masallaci Mai Alfarma, zuwa Masallaci Mai Nisa, wanda muka sanya albarka a gefensa, domin mu nuna masa daga ayoyinmu, lallai ne shi, shi ne Mai ji, Mai gani" [Isra'i: 1].
Kuma lallai lokaci ya yi, wanda dukkan duniya zata sani, lallai lokaci ya yi, wanda dukkan duniya za su sani, cewa lallai wurin da aka yi isra'i da Annabinmu Muhammadu (صلى الله عليه وسلم) wuri ne, na dukkan masu tauhidi, a ko-ina suke a duniya, wuri ne na wadanda suka fadi LA ILAHA ILLAL LAHU, MUHAMMADUR RASULUL LAHI.
Kuma masarautar Larabawa ta Saudiya ta kasance kuma ba za ta gushe ba, tana tsaye, kuma baza ta taba ja-da baya ko ta nisanci manufofinta da halayenta na musulunci da 'dan'adamtaka ba, a kan lamarin Falasdinu, da Kudus wadanda aka mamaye, Kuma za ta ci gaba da ayyukanta da izinin Allah, wajen warware wannan matsalar, da kuma taimaka wa wanda aka zalunta.
Kuma rayukanmu natsattsu ne da alkawarin Allah, domin duk yadda makiya suka yi karfa-karfa, to ita kuma nasara tana tare da muminai masu hakuri. Kuma lallai wannan masallacin yana da Ubangijinsa wanda zai kare shi,
"Kuma hakika mun rubuta a cikin littatafain baicin Lauhul mahfuz, cewa lallai kasa, Bayina salihai suke gadonta" [Anbiya'i: 105].
Ya Allah! Ka kiyaye Kudus madaukaki, kuma ka dawo da shi cikin kulawar musulunci da musulmai, Ya Allah ka daukaka musulunci da musulmai
Bayin Allah
"Lallai ne, Allah da Mala'ikunsa suna yin salati ga wannan annabin, Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi salati a gare shi, da sallama ta aminci" [Ahzab: 56].

,,,          ,,,          ,,,

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...