2019/11/28

TSAWATARWA DAGA ASKE GEMU (التحذير من حلق اللحية)


TSAWATARWA DAGA ASKE GEMU
(التحذير من حلق اللحية)
Na Shehun Malami Muhammadu dan Salih Al-usaimin
Allah ya yi masa rahama

Tarjamar Abubakar Hamza
Aske gemu haramun ne, saboda saba wa Manzon Allah ne  (S.A.W), domin Annabi (S.A.W) ya ce: "Ku cika gemu, ku rage gashin baki". Kuma saboda askwar ficewa ne daga shiriyar Manzanni, zuwa ga shiriyar masu bautar Wuta (Majusawa) da Mushirkai.
IYAKAR GEMU (LIHYAT) –Kamar yadda masanan harshen Larabci suka fada- shine: Gashin da ya tsiro a fiska, da muka-mukai biyu, da kumatu biyu; Ma’anar wannan shine: Duk abinda ya tsira a jikin kumatu biyu, ko a muka-mukai biyu, da haba, to wannan yana daga cikin gemu (lihyat). Kuma cire wani abu daga cikin hakan ya shiga cikin sabo, domin Annabi (S.A.W) ya ce: "Ku cika gemu", "Ku sake gemu", “Ku tara gemu”,  Ku ajiye gemu”. Wadannan kuma sai suka nuna cewa, lallai bai halatta a cire wani abu daga jikin gemu ba. Saidai saboda kasancewar sabo mataki-mataki ne, sai aske gemun gaba dayansa yafi muni, akan yanke wani abu daga jikinsa, domin askewan yafi girma kuma yafi rage shi nuna sabawar mai aikata hakan ga Sunnah. Wannan kuma shine gaskiya, kuma ita ce, tafi cancantar a bi ta.
Kuma ka tambayi kanka: Mai zai hana ni karbar gaskiya, da yin aiki da ita, domin yardar da Allah tare da neman ladansa? Don haka, kada ka fifita son rai, da ganin damarka,ko abinda abokai suke so, akan yardar Ubangijinka, Allah Ta’alah ya ce: "Amma wanda ya ji tsoron tsayuwa ga UbangijinSa, sai ya hana ransa abinda take so * To lallai Aljannah ita ce, makoma a gare shi” [40-41].
Shi kuma rage gashin gemu, ya saba wa abinda Annabi (S.A.W) ya bada umurni a cikinj fadinsa:  Ku tara gemu”,  "Ku bar gemu", "Ku sake gemu"; Don haka, Wanda ya so bin umurnin Manzon Allah (S.A.W) da bin shiriyarsa (S.A.W), to kada ya ciri wani abu daga gemunsa; domin shiriyar Manzon Allah (S.A.W) ita ce, kada Mutum ya cire wani abu daga gemunsa. Kuma hakan (wato tara gemu) ita ce shiriyar Annabawan da suka gabace shi, saboda dukkanmu mun karanta fadin Allah Ta’alah dangane da Haruna ga annabi Musa: "Ya dan mamata: Kada ka kama min gemuna, ko kaina". Wannan kuma dalili ne akan cewa, lallai Annabi Haruna yana da gemun da za a iya damkewa. Kuma hakan shine shiriyar cika-makon annabawa; Muhammadu (S.A.W) domin gemunsa ya kasance mai tarin yawa, cikakkke. Don haka; Duk wanda ya so ya bi Annabi cikakken bi, ya kuma  bi umurninsa sau da kafa, to kada ya aske komai daga gemunsa; ta fiskar tsawonsa ko fadinsa.
Wasu Mutane a farkon farin fitowar gemunsu, ya kan kasance gashi ne a rarrabe, sai Mutum ya ce: zai aske shi, domin gashin su fito gaba daya a tare. Wannan kuma ba daidai ba ne; saboda Mutum zai iya askewan, ya zama ya saba umurnin Annabi (S.A.W) da aikata hakan, sai kuma ya mutu gabanin sake tsirowar gemun. Wajibin shine ya bar gemun kamar yadda ya kasance,saboda idan gemun y agama girmansa ko fitowansa, to ya kan taru cikin yanayi mai kyau.
Allah ne Mai datarwa ([1]).


([1]) MAJMU’U FATAWA WA RASA’LIL USAIMIN, (11/ 125-126).

1 comment:

  1. Your Affiliate Profit Machine is waiting -

    And making money with it is as easy as 1---2---3!

    This is how it all works...

    STEP 1. Input into the system which affiliate products the system will promote
    STEP 2. Add some push button traffic (this LITERALLY takes 2 minutes)
    STEP 3. Watch the system grow your list and sell your affiliate products for you!

    Are you ready to start making money???

    Click here to launch the system

    ReplyDelete

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...