2019/01/03

Huzaifiy HUDUBAR 28 Rabiyus Saniy 1440H daidai da 4 Janairu 2019M daga MASALLACIN ANNABI SAW












HUDUBAR MASALLACIN ANNABI
(صلى الله عليه وسلم)
JUMA'A, 28/RABIYYUS SANIY/1440H
daidai da 4/JANAIRU/ 2019M




LIMAMI MAI HUDUBA
SHEIKH ALIYU BN ABDURRAHMAN ALHUZAIFIY





TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
RAYUWAR DUNIYA
(عمر الإنسان)
Shehin Malami wato: Aliyu bn Abdurrahman Alhuzaifiy –Allah ya kiyaye shi- ya yi hudubar juma'a mai taken: RAYUWAN DAN ADAM, Wanda kuma a cikinta ya tattauna, akan

بسم الله الرحمن الرحيم
HUDUBAR FARKO

Yabo ya tabbata ga Allah; Mabuwayi Mai yawan gafara, Yana shigar da dare akan yini, kuma yana shigar da yini akan dare, kuma kowane abu a wurinSa yana da wani gwargwado. Ina yin yabo ga Ubangijina kuma ina gode masa akan ni'imominSa da falalolinSa.
Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya, sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya, Makadaici Mai rinjaye.
kuma ina shaidawa lallai annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawanSa ne ManzonSa zababbe,
Ya Allah! ka yi dadin salati, da sallama da albarka ga bawanka kuma Manzonka; Muhammadu, da iyalansa da sahabbansa zababbu,

Bayan haka:
Sai ku yi takawar Allah Madaukaki kuma ku masa biyayya, domin yin da'a a gare shi, shine hanya mafi mikewa kuma mafi karfi, kuma ku rika guzuri ga lahirarku, domin mafi alherin guzuri shine tsoron Allah!

Ya ku, Bayin Allah !!!
Ku rika tunani kan lokaci dan kadan wanda aka dibar ma Duniya, da kayan kawanta wulakantacce, da yadda halayenta suke yawan jujjuyawa, sai ku gane ko ku riski matsayin Duniyar, kuma ku san sirrinta, domin duk wanda ya amintu da ita, to lallai shi rudadde ne, kuma wanda ya amintu da ita, to lallai shi halakakke ne.
Kuma karancin shekarun da aka dibar wa Duniya ya ta'allaka ne da karancin shekarun da aka diba wa Mutum a cikinta.
Kuma rayuwar Mutum tana farawa ne da awanni, bayan awowi kuma sai kwanaki, bayan kwanaki kuma sai watanni, bayan watanni kuma sai shekara, bayan shekara daya kuma sai shekaru, Sa'annan sai rayuwar Mutum gaba daya ta kare. Kuma Mutum baya sanin abinda zai gudana a bayan mutuwarsa na manya-manyan lamura. Kuma shin rayuwar wanda su ka zo a bayanka -Ya kai Mutum- rayuwarka ce?
Kuma rayuwar kowace halitta, bangare ne na rayuwar al'umma gaba daya.
Kuma ita Duniya dan mata'i ne, kuma ma'anan mata'i shine dan abinda ake jin dadi da shi, a lokacinsa, sa'annan sai ya kare a wannan lokacin, Allah Ta'alah ya ce: "Kuma lallai wannan rayuwar dan jin dadi ne, kuma lallai Lahira ita ce gidan tabbata" [Gafir : 39].
Kuma Allah Ta'alah ya ce: "Kuma ka buga musu mislain rayuwar Duniya,kamar Ruwa ne wanda muka saukar da shi daga sama, sa'annan tsirin kasa ya gauraya da shi, sa'annan ya wayi gari yana duddugagge, iska tana shikarsa, Kuma Allah ya kasance Mai yawan ikon yi ne akan dukkan komai" [Kahf: 45].
Kuma Allah Subhanahu ya ce:  "Kuma, ka bada labari, idan muka jiyar da su dadi a shekaru! * Sa'annan abinda suka kasance ana musu wa'adi ya je musu * abinda suka kasance ana jiyar da su dadin, ba zai tunkude azaba daga gare su ba!" [Shu'ara'i: 205-207].
Kuma Ubangijinmu Mabuwayi da daukaka ya bamu labari, kan gajartan zaman Mutane a cikin kabarinsu har zuwa lokacin da za a tayar da su domin hisabi, da cewa wannan lokaci mai tsawo kamar wani dan yanki lokaci ne takaitacce, Allah Ta'alah ya ce: "Kuma ranar da zai tara su, kamar ba su zauna ba face sa'a guda daga yini, wanda suke sanayya da juna a cikinsa" [Yunus: 45].
Kuma Allah Ta'alah ya ce: "Kuma ka yi hakuri, kamar yadda karfafan niyya daga Manzanni suka yi hakuri, kuma kada ka yi musu gaggawa, Kamar dai su a ranar da suke ganin sakamakon abinda aka musu wa'adinsa, ba su zauna ba, face sa'a guda daga yini, isarwa (dai da Manzanci), Kuma babu wanda za a halakar face Mutane fasikai" [Ahkaf: 35].
Kuma Allah Ta'alah ya ce: "Kuma a ranar da sa'a ke tsayuwa, masu laifi na rantsuwa, ba su zauna (a cikin kabari) ba face sa'a guda" [Rum: 55].
Don haka, nawa ne shekarunka -Ya kai wannan Mutum-, daga cikin wannan sa'ar wanda Allah Ta'alah ya bamu labarin cewa, shine dan lokacin da aka dibar wa Duniya, a lokacin da kiyama zata tsayu!
Kuma ita wannan sa'ar wanda ita ce lokacin da aka dibar wa Duniya, kamar wani bantare ne (karami) ko digo daya na ruwa daga tekun zamani na har abada!

Don haka,
Abin yabo, yana tabbata ga wanda ya yi aikin kwarai a cikin rayuwarsa takaitacciya, kuma ya kaurace wa ayyukan haram, kuma ya kiyayi bin soye-soyen zuciya, da hanyoyin zamiya da bacewa, sai ya rabauta a cikin rayuwarsa da aikata alkhairori,  kuma ya rabautu bayan mutuwarsa da samun yardar Allah a cikin ni'imomin Aljannah!
Kuma bone ya tabbata, ga wanda ya bi ye wa sha'awowinsa, kuma ya tozarta salloli da ayyukan wajibai, kuma ya yi ta aukawa cikin zunubai masu halakarwa, har ya fada cikin ramukan Jahannama, sai abincinsa ya kasance itaciyar zakkum (na danyen wuta), abin shansa kuma ya kasance surkin jini (wato, diwa) da tafasasshen ruwa (ruwan zafi),
Ya wanda lafiyarsa ta sanya shi dagawa, sai ya rika aikata sabo!
Ya wanda faragar lokacinsa ya lalata shi sai ya yi ta wasa da wargi!!
Ya wanda dukiyarsa ta fitine shi, sai ya gangara cikin wuta!!!
Ya wanda ya biye wa son zuciyarsa sai ya tuntsura kuma ya fadi!!!!
Ya wanda samartakarsa ta rude shi, sai ya mance da tsufa!!!!!
Ya wanda ya yi amfani da ni'imomin da Allah ya masa sai yake taurin kai da dagawa!!!!!!
Shin ba ka san cewa, Allah babu wani abu a cikin sama da kuma a cikin kasa wanda yake gagaransa ba? kuma lallai shi, Mai tsananin ukuba ne!
Shin baka da yakini kan mutuwa ne, da abinda yake bayanta na hisabi!
Ya wanda nisan ajali ya sanya shi tsaurin kai ga UbangijinSa! Haka batun samun burinsa! Har mutuwa ta fizge shi! Ta yaya irin wannan zai samu damar komawa Duniya domin ya gyara aiki!!
Shin lokaci, bai yi ba, Ya kai gafalalle, mai bijirewa, mai sabo, wanda a cikinsa zaka tuba ga Ubangijinka ka kuma mayar da lamari zuwa gare shi!
Shin lokacin da zaka farka daga irin wannan kurmar gafala, bai yi ba! Sai ka amsa wa Ubangijinka!!
Shin baka da abin lura, cikin lamarin karnuka masu karfi wadanda suka shude, da wuraren zamansu wofantattu, bayan sun daddasa nau'oin bishiyoyi, sun gudanar da koramai, sun gina biranai! Yaya suka kasance bayan gini sai dai alama, kuma bayan daukaka sai labari!!!  Kuma yaya aka dauke su daga benaye zuwa kaburbura! Sai suka wayi gari suna jingine da ayyukansu, Sai ma'abuta kyawawan ayyuka suka zama sune masu samun babban rabo, ma'abuta munana kuma, sune masu yin hasara da nadama!
Shin mutuwa, akwai mai tunkude ta?
Shin akwai mai shiryatarwa, in banda Alkur'ani?
Lallai cikin fiskantowar yini da shekara, da juyawan wani yinin da shekara, akwai abin dubawa, saboda duk yinin da ka bar shi bayanka, to ba zai dawo ba, kuma wani yinin kake fiskanta, har ajali ya kare, buri kuma ya yanke! Allah Ta'alah ya ce: "Kuma Mutum bashi da komai face abinda ya aikata * Kuma lallai aikinsa za a ganshi * Sa'annan a saka masa da sakamako mafi cikar ma'auni * Kuma lallai, makoma izuwa ga Ubangijinka kawai take!" [Najm: 39-42].
Sai ka yi aiki domin gidan dawwama, wanda ni'imarta baya karewa, kuma baya raguwa, sai ma karuwa! Samarin wannan gida tsufa bata zuwa musu, kuma basu tsoron cutuka, Allah Ta'alah yana fada akanta: "Ku shige ta da aminci, waccan ita ce ranar dawwama * suna da abinda suke so a cikinta, kuma tare da mu akwai karin ni'ima" [Kaf: 34].
Kuma Allah Ta'alah ya ce: "Ku shiga Aljannah ku da matan aurenku ana girmama ku * Ana kewayawa akansu da akussa na zinariya da kofuna, alhali kuwa a cikinsu akwai abinda rayuka suke marmari, kuma idanu su ji dadi, kuma ku a cikin Aljannar madawwama ne * Kuma waccar ita ce Aljannar, wannan da aka gadar da ku ita, saboda abinda kuka kasance kuna aikatawa * Kuna samun kayan marmari masu yawa a cikinta, daga cikinsu kuke ci" [Zukhruf: 70-73].
Kuma ku ji tsoron Wutar da ba a sassauta azaba ga ma'abutanta, ta hanyar aiki da umurnin Allah mai karfi, da nisantar fushinsa mai tsanani, Allah Ta'alah ya ce: "Kuma wadanda suka kafirta an yanka musu wadansu tufafi daga wata irin wuta, ana zuba tafasasshen ruwa daga saman kawunansu * Da shi ake narkar da abinda yake a cikin cikunansu, da fatun jikinsu * Kuma suna da wadansu gudumomin duka na bakin karfe * A duk lokacin da suka yi nufin fita daga gare ta, saboda bakin ciki, sai a mayar da su a cikinta, (a ce musu): Ku dandani azabar gobara" [Haj: 19-22].
Sai ku yi aiki -Ya ku bayin Allah- domin wannan Aljannar madaukakiya! Kuma ku nisanci zunubai, wadanda suke wurga ma'abutansu cikin Wutar Hawiya mai zafi.
Kuma ku sani, lallai babu komai tsakanin Mutum da shiga Aljannah ko Wuta, face mutuwa, An rawaito daga Abu-hurairah -Allah ya kara yarda a gare shi-, daga Annabi -sallal Lahu alaihi wa sallama- ya ce: "Ku rigayi abubuwa bakwai da ayyuka, Shin wani abu kuke jira face, Talauci me mantarwa, da wadaci mai sanya dagawa, ko cuta mai lalatawa, ko  tsufa mai kararwa, ko mutuwa mai daukewa, ko zuwa Dujjal, mafi sharrin wanda ake jira, ko kuma zuwan kiyama, kuma zuwan sa'arta shine yafi tsananin masifa, kuma mafi daci", Tirmiziy ya ruwaito.
Kuma ya zo cikin wani hadisi cewa: "Ku yawaita ambaton mai yanke jin dadi, wato mutuwa, domin ba a ambaton mutuwa ga abu mai yawa face ta karanta shi, ko kuma ga kadan face ta yawaita shi".
Kuma Annabi -sallal Lahu alaihi wa sallama- ya ce: "Ya isa mutuwa ta zama babban mai wa'azi ".
-Ya kai Musulmi- Sai ka yi bankwana da ranakunka, da abinda ka samu ikon kunshe shi a cikinsu na kyawawan ayyuka, kuma ka kiyaye takardun rubuta ayyukanka daga munanan ayyuka, Allah Ta'alah ya ce: "Kuma ku gabatar da alheri saboda kanku, kuma ku bi Allah da takawa, kuma ku sani cewa lallai ne ku masu haduwa ne da shi, kuma ka bayar da bushara ga muminai" [Bakara: 223].
Kuma ya ce: "Kuma ku tsayar da sallah, ku bada zakkah, kuma duk abinda kuka gabatar da shi ga kawunanku na alheri za ku same shi a wurin Allah, yana mafifici, kuma zai fi girma ga sakamako" [Muzzammil: 20].
Allah ya mini albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai girma, ,,,.
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,
HUDUBA TA BIYU
Yabo ya tabbata ga Allah wanda ya san sirri da abinda yafi buya, tsayayye akan kowace rai da abinda ta aikata, yana kididdige ayyuka, kuma yana yin sakamako akansu da mafi cikan ma'auni,
Ina yin yabo ga Ubangijina kuma ina gode masa, kuma ina tuba zuwa gare shi ina neman gafararSa,
Kuma ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, yana da sunaye mafiya kyawu.
Kuma ina shaidawa lallai annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawanSa ne manzonSa zababbe,
Allah ka yi dadin salati a gare shi da iyalansa da sahabbansa ma'abuta hakuri da takawa,
Bayan haka
Ku ji tsoron Allah iyakar takawarsa, kuma ku yi riko a Musulunci da igiya mai karfi,
Ya ku Bayin Allah
Lallai Allah ya bude muku kofofin rahama, da abinda ya shar'anta muku na aikata alkhairori, da nisantar laifuka ababen kyama,
Don haka, kada wani Mutum ya toshe kofar rahama ga kansa, ta hanyar yakar Allah da aikata zunubai, Saboda ALlah Ta'alah yana cewa: "Kuma rahamata ta yalwace dukkan komai, sa'annan zan rubuta ta ga wadanda suke yin takawa, kuma suna bayar da zakka, da wadanda suke a game da ayoyinmu muminai ne" [A'araf: 156].
-Ya kai wannan Bawa- ka ribaci zamanin lafiya (gabanin zuwan cuta), saboda an rawaito daga Abdullahi dan Abbas -Allah ya kara yarda a gare su- ya ce: "Ni'imomi biyu mafi yawan Mutane basu ribatarsu; lafiya da faragar lokaci".
Kuma an ruwaito daga Abdullahi dan Umar -رضي الله عنهما- ya ce: Manzon Allah -صلى الله عليه وسلم- yana cewa: "Ka kasance a Duniya kamar wani bako, ko kuma mai ketare hanya,,,,".
Ya ku Musulmai
"Lallai ne Allah da Mala'ikunSa suna yin salati ga wannan Annabi, ,,," [Ahzab: 56].

2018/12/22

HUDUBAR dr. Salah dan Muhammadu Albudair, 14 RABIYYUS SANIY 1440H daidai21 Disemba 2018M











HUDUBAR MASALLACIN ANNABI
(صلى الله عليه وسلم)
JUMA'A, 14/RABIYYUS SANIY/1440H
daidai da 21/DISEMBA/ 2018M


LIMAMI MAI HUDUBA
SHEIKH DR. SALAH DAN MUHMMADU ALBUDAIR



TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
KYAUTATA LADABI
(حسن الأدب)
Shehin Malami wato: Salah bn Muhammadu Albudi–Allah ya kiyaye shi- ya yi hudubar juma'a mai taken:LADABI,Wanda kuma a cikinta ya tattauna, akan

بسم الله الرحمن الرحيم
HUDUBAR FARKO
Yabo ya tabbata ga Allah wanda ya tarbiyantar da mu da Alkur'ani da Sunnah da mafi kyan ladabi, kuma ya saukar da mu ga bazarar falalarSa mai yabanya, kuma ya ajiye mu cikin yalwar falalarSa mai fadi.
Kuma ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; shi kadai yake bashi da abokin tarayya, zuwa gare shi nake kira, kuma a gare shi nake mayar da lamura.
Kuma ina shaidawa lallai annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawanSa ne kuma manzonSa, an turo shi domin ya cika kyawawan halayya, kuma sune matsayi mai girma.
Allah, ya yi dadin salati da sallama a gare shi da iyalansa da sahabbansa, salatin da zamu samu cikakken lada da shi, da mafi girman rabo.
Bayan haka:
Ya ku Musulmai
Ku ji tsoron Allah; domin mai takawa ya kan samu babban rabo, kuma mabarnaci shakiyyi ya yi hasara,  "Ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah iyakar tsoronsa, kuma kada ku mutu face kuna Musulmai" [Ali-imraana: 102].

Ya ku Musulmai
Samun daukakar Musulmi shine ladabinsa, kuma ladabi madaukaki yana wadatarwa daga matsayi  madaukaki da danganta madaukaki, saboda samun daukaka yana cikin himmomi madaukaka, ba daga dangantaka ko kasussuwan (iyaye da kakanni) da suka rududduge ba.
BAI CUTAR DA WANDA YA TATTALI LADABI DA HANKALI BA,
KASANTUWAR BAI FITO DAGA KABILAR ABDU-MANAFI BA

Falala cikakkiya itace ladabi ya kasance tabbatacce a cikin iyaye, sai kuma ya samu gindin zama a cikin 'ya'yansu da jikoki;
SUN KAWATA TSOFONSU DA KYAKKYAWAN NA ZAMANINSU,
DA KUMA HALAYEN GIRMA, DA KYAWAWAN DABI'U

MADALLA DA MUTANEN DA KAI NE RESHEN TUSHENSU,
KUMA MADALLA DA KAI, DOMIN DAGA ASALINSU RESHENKA YA SAMU

LADABI shine yin abin yabo; cikin zance da aiki.
Kuma Ladabi shine, aikata ababe masu falala, da barin masu muni.
Kuma shine, girmama na sama da kai, da tausasawa na kasa.
Kuma Ladabi shine, riko da kyawawan dabi'u, Allah Ta'alah yana cewa: "Kuma lallai kai kana kan wasu halaye masu girma" [Kalam: 4].
Adiyyatul Aufiy ya ce: "Wato, lallai kai kana kan ladabi mai girma".
Ladabi shine takawar Allah Ta'alah, da yin da'a a gare shi, da nisantar saba masa.
NA YI TARBIYYA GA KAINA, SAIDAI BAN SAMA MATA
LADABI BA, IDAN BA A CIKIN TAKAWAR ALLAH BA.
Mujahid –Allah ya yi rahama a gare shi- ya ce, alhalin yana tafsirin: "Ku kare kanku da iyalanku daga wata wuta" [Tahrim: 6], wato: "Ku yi wasiyya ga kanku da iyalanku da takawar Allah, kuma ku ladabtar da su".
YIN TARBIYYA A SANNU-SANNU, HAKIKA YANA AMFANAR KANANAN YARA
SAIDAI A BAYAN GIRMA, YIN TARBIYYA (A GALIBI) BAYA WANI AMFANI

SABODA RESSAN DANYEN BISHIYA IDAN KA NEMI DAIDAITA SU, SUKAN MIKE
AMMA BASU YIN TAUSHI IDAN KA NEMI DAIDAITA SU BAYAN SUN ZAMA ITACE (BUSASSHE)

KYAU BA SHINE, TUFAFIN DA SUKE KAWATA MU BA,
LALLAI KYAU (NA HAKIKA) SHINE KYAN ILIMI DA LADABI

Kuma an yi wa ladabi sunan ladabi ne, saboda yana ladabtar da Mutane ya dora su akan abubuwan yabo, ya kuma hana su aikata munanan ayyuka.
Ladabi shine, kyautata magana, da kyan zance, da dadinsa, da kyautata shirya zance, da kwarewa cikin mu'amala, da kula da kyan yanayi (na tufafi), da gyaran zuciya da gangar jiki.
Ladabi (wato أدب) ba kawai shine fasaha da balaga da hardace ilmuka da wakokun Labarawa ba, Saidai hakikanin ladabi shine sifantuwa da kyakkyawan halaye.
Da yin farin ciki da abinda Allah ya yi ga wani na ni'ima, da nisantar hassada, da kubuta daga dabi'ar kyashi.
Duk wanda hankalinsa ya cika, ladabinsa da tarbiyyansa suka zama kawa a gare shi, sai maganarsa tayi karanci, sai shirunsa ya yawaita, lafazinsa ya yi kyau, hakurinsa ya bayyana.
SAI KA KASANCE MAI KARAMCI, MAI HAKURI, MAI HANKALI, FADAKAKKE,
MAI TSAFTAR HALAYE, DAGA WAUTA, DA FUSHI

KA KIYAYE HARSHENKA, DAGA ZAMBO, DA WAUTA,
DA KUMA ABOTAR SAKARKARU, KA NISANCI KARYA.

Ana cewa: Dabi'u guda uku, Mutum a tare da su baya zama bako: Nisantar wadanda ake zargi, da kyakkyawan ladabi (tarbiyya), da nisantar cutarwa.
YANA KAWATA BAKO A YAYIN BAKUNCINSA
DABI'U GUDA UKU; DAGA CIKINSU AKWAI KYAUTATA LADABI

NA BIYUNSU: SHINE KYAUTATA DABI'ARSA,
NA UKUNSU KUMA, NISANTAR WURAREN ZARGI
IbnulKayyim –رحمه الله- ya ce: "Ladabin Mutum shine tambarin samun sa'idarsa da nasararsa, Shi kuma karancin ladabinsa shine tambarin tabewarsa da halakarsa, domin ba a iya janyo alherin Duniya da lahira da sai da ladabi. Kuma ba a janyo talaucin Duniya da lahira sai da dabi'ar karanta ladabi. Ka duba lamarin ladabi ga iyaye biyu; yadda ya tseratar da Ma'abucinsa daga zaman kogo a lokacin da dutse ya sauko akansu, kuma ka yi dubi ga ladabin Abubakar siddik -Allah ya yarda da shi- ga Annabi -sallal Lahu alaihi wa sallama- a lamarin sallah, wato lokacin da ya ki ya shiga gabansa, kuma ya ce: BAI DACE GA IBNU-ABIY KUHAFAT, YA SHIGA GABAN MANZON ALLAH -SAW-, yadda hakan ya gadar masa da samun matsayinsa da jagorantar al'umma a bayansa". Maganarsa ta kare.

LALLAI NE NI, DABI'U MASU KARAMCI SUNA FARANTA MIN,
IRIN FARIN CIKIN BAKO A LOKACIN DA YA KOMO, YA SADU DA MASOYANSA

KUMA YIN TUNANI KAN MUTUNTAKA DA KYAUTA A CIKIN JERIN KYAWAWAN HALI
YANA JIJJIGA NI, JIJJIGAWAR MUTUMIN DA KE CIKE DA SHAUKI

IDAN AKA AZURTAKA DA DABI'A ABAR YABO,
HAKIKA MAI RABIYAR ARZIKI, SHINE YA ZABE KA

MUTANE, WANNAN RABONSA DUKIYA, WANNAN KUMA
ILIMI, WANNAN KUMA KYAWAWAN DABI'U

SHI ILIMI, IDAN DABI'UN DA ZASU DAUKAKA SHI BASU DABAIBAYE SHI BA,
SAI YA KASANCE ABIN HAWAN ZILLEWA,

KADA KA YI ZATON ILIMI ZAI YI AMFANI, SHI KADAI
MATUKAR MA'ABUCINSA BAI YI KAWA DA DABI'U BA

SAU NAWA MAI ILIMI YA SHUMFUDA IGIYOYIN ILIMI
DOMIN CIN MUTUNCIN MUTANE, DA YANKE ZUMUNTA, DA RARRABA KAI!

SHI KUMA MALAMIN WASU MUTANE YA RIKA KAFA FIKIHUNSA
DOMIN MAKIRCI, KO YA ZAMA MAI NEMAN HALATTA SHIKA!

UWA KUMA, MAKARANTA CE, IDAN KA TATTALE TA,
TO, KA YI TATTALIN AL'UMMA, MAI KYAWUN HALAYE!

UWA DAUSAYI CE, IDAN AKA BITA DA BAYIN RUWA,
SAI DAUSAYIN YA BADA YABANYA DA CIKAKKEN GANYE

UWA ITACE MALAMAR MALAMAN DA FALALARSU
TA CIKE SARARIN SAMANIYAR DUNIYA

KU YI TARBIYYA TAGARI GA 'YA'YANKU MATA
DOMIN NAGARTA SHINE MAFI ALHERIN ABIN RIKEWA

YANA  WAJABA 'YA'YANKU MATA SUSAN
HASKEN SHIRIYA, KUMA SU SAN KUNYA
Kuma hakika, littatafan sihah da sunan da musannafaat, sun bada kulawa wajen tattaro hadisai, kuma babu wani littafi daga cikin wadannan littatafan masu girma wadanda ake daukansu a matsayin madogarar ma'abuta Musulunci, face mawallafinsa ya ware littafin ladabi, ko babi-babi akan ladibi, Duba littafin ladabi a cikin sahihul Bukhariy, da littafin ladabi a cikin sahihu Muslim, da littafin ladabi a cikin sunan na Abu-dawuda, da littafin ladabi a cikin sunan na Tirmiziy, domin ka yi mamakin girman ladabi a cikin addinin Musulunci, da matsayinsa a cikin sunna da shari'a.

Kuma yana daga manyan sunnoni a babin ladduba da halayya: Abinda aka ruwaito daga Abu-Umamah Albahiliy -رضي الله عنه-, ya ce: Manzon Allah -صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Lallai ni na lamunce da bayar da gida a gabar Aljannah ga wanda ya bar jayayya, koda yana da gaskiya. Da wani gidan a tsakiyar Aljannah ga wanda ya bar karya koda a cikin wasa ne. Da wani gidan a kololuwar Aljannah ga wanda ya kyautata halayensa", Abu-dawud ya ruwaito shi.
Abdullahi bn Almubarak ya ce: "Mu, lallai mun fi bukatar kadan daga ladabi fiye da ilimi mai yawa".
Imamu Maliku ya ce: "Mahaifiyata ta kasance tana daura min rawani, sai ta ce: Ka tafi ga malam Rabiy'ah, ka koyi ladabinsa gabanin koyan iliminsa".
Abdullahi dan Wahaf ya ce: "Abinda muka koya na ladabin Maliku yafi abinda muka koya na iliminsa".
Isma'il dan Ulayyah ya ce: "Lallai a majalisar Imamu Ahmad Mutane dubu biyar suna taruwa, ko hakan da doriya, kuma kamar dari biyar, suna rubuta iliminsa, sauran kuma suna koyan kyakkyawan ladabinsa, da halayya".
Kuma Alkhadib Albagdadiy -رحمه الله- ya ce: "Wajibi shine daliban hadisi su kasance sun fi sauran Mutane cikar ladabi, da tsananin tawali'u, kuma su fi su tsantseni da riko da addini, kuma sufi karancin wauta da fushi, wannan kuma saboda hadisan da suka kunshi kyawawan halayyar Manzon Allah -صلى الله عليه وسلم- ko-yaushe sukan  kwankwasa kunnuwansa, da batun laddubansa, da tarihin magabatan kwarai, daga iyalan gidansa da sahabbansa, da hanyoyin Maluman hadisi, da labarun falalar Mutanen baya, sai dalibin hadisi ya yi aiki da abinda yafi kyau yafi dacewa, ya kuma kauce wa munanan hanyoyi da ayyuka".

Ina fadar abinda kuke ji, kuma ina neman gafarar Allah; sai ku nemi gafararSa, lallai ne shi ya kasance ga masu  komawa gare shi, Mai yawan gafara.
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,

HUDUBA TA BIYU
            Yabo ya tabbata ga Allah wanda ya bada mafaka ga wanda ya nemi fakewa ga tausasawarSa,
            Kuma ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, ya bada lafiya cikin ni'imtarwarsa, ga wanda ya debe tsammanin samun waraka daga cutukansa.
            Kuma na shaida lallai shugabanmu kuma annabinmu Muhammadu bawansa ne manzonsa, wanda ya bi shi ya shiryatu ya dau hanya, wanda kuma ya saba masa ya bata ya bar turba,
            Allah ya yi dadin salati a gare shi da iyalansa da sahabbansa,  salati mai ninkuwa, da sallama mai wanzuwa,
Bayan haka
Ya ku Musulmai
Ku ji tsoron Allah kuma ku kiyaye shi, kuma ku yi da'a a gare shi kada ku saba masa, "Ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah kuma ku kasance tare da masu hakuri" [Tauba: ].

Ya ku Musulmai
Ku yi godiyar ni'imar Allah akanku, Lallai ya turo muku da iska masu albishir, da girgije masu nauyi, masu barin ruwan sama, girgije bayan girgije, da suka sassauka a cikin kwari masu jin kishi, da saharori masu wahalar samun ruwa, da kuramen duwatsu daskararru, wanda tuni rashin ruwan ya jigata su, ,,, sai suka jijjika da ruwan sama,  sai gashi kasarku -da falalar Allah- tayi ciyawa, sai dausayinku ya zama abin kaye da saukan wannan ruwan, duwatsunku suka yi kore da rahamar Allah, a cikin shekararku da ta cika da yabanya, da wani yanayi mai kyau mai kayatarwa, wanda yake nuni kan ikon Allah da hikimarSa da rahamarSa da yalwar falalarSa, da arzikinSa da kyautatawarSa.

HAR LOKACIN DA DAUSAYI YA RUNGUME KASA
SAI CIYAWAR FARKO-FARKO MASU KARFAFAR JUNA SUKA FUFFUDO

AKAN KASA DAYA, SAI SUKA ZAMTO KAMARSU DAYA TA FISKAR KYAWU
YAYIN DA TA FISKAR LAUNUKA BASU ZAMTO ABU DAYA BA

IDANUNKA NA NUNA MAKA IDANIYAR RUWA
MASU KYAU DA DADI, WANDA SUKA FI IDANIYAR YANKIN JA'AZIRI

BA ABINDA YAFI KYAN GANI, IN KA ZIYARCE SU,
KO KA GA HAKIKANINSU, NA KYAN DAUSAYI KORE

IDAN KA JE MUSU, SAI SU BAKA GANI MAFI KYAWU, IDAN KUMA BAKA JE BA,
SAI YA ZIYARCE KA CIKIN DADDADAR ISKAR DA TAKE ZUWA DA SAFIYA

Sai ku buda idanuwanku cikin kyawun halittar Allah Ta'alah, tare da kula da ladduban fita yawon buda ido, kuma kada ku bata, ko ku sanya najasa a wuraren da Mutane suka rike su a matsayin inuwowin zama, da kailula, haka wuri mai dausayi da ciyawoyi, ko karkashin bishiya mai 'ya'ya, ko wurin diban ruwa, ko hanyar da ake binta da kafa, ko da dabbobi, ko da motoci. saboda an ruwaito daga Abu-hurairah -رضي الله عنه-, lallai Manzon Allah -صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Ku kiyayi wuraren tsinuwa guda biyu, Sai suka ce: wadanne ne wurare biyu na la'ana Ya Ma'aikin Allah! Sai ya ce: Wanda yake biyan bukata akan hanyar Mutane ko inuwarsu", Muslim ya ruwaito.
Kuma an ruwaito daga gare shi, رضي الله عنه ya ce: lallai Manzon Allah -صلى الله عليه وسلم- ya ce: "Wanda ya yi kashi a hanyar da ba matacciya ba, daga cikin hanyoyin Musulmai, to tsinuwar Allah ta tabbata a kansa, da ta Mala'iku, da ta Mutane gaba daya", Baihakiy ya ruwaito.
 Sai ku yi salati da sallama ga …………………………

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...