2015/12/28

ملحص خطبة يوم 14 من ربيع الأول 1437هـ بالمسحد النبوي في موضوع: القرآن الكريم، فضله وفضل حمله


ملحص خطبة يوم 14 من ربيع الأول 1437هـ بالمسحد النبوي في موضوع: القرآن الكريم، فضله وفضل حمله
ألقى فضيلة الشيخ الدكتور عبد المحسن القاسم على منبر رسول الله صلى الله عليه وسلم خطبة الجمعة في هذا اليوم 14/ ربيع الأول / 1437هـ الموافق: 25/12/ 2015م، وتناول فيها موضوع: القرآن الكريم وأنه كلام الله العظيم؛ وذكر الخطيب طائفة كبيرة مِن فضائله، ومكانة حملته، وبيَّن في مقدمتها أنّ الله تعالى يتصف بصفات جمة، منها: صفة الكلام، وأنه يتكلم بما شاء إذا شاء متى شاء، وأنه لا منتهى لكلماته، (قل لو كان البحر مدادًا لكلمات ربي لنفد البحر قبل أنْ تنفد كلمات ربي ولو جئنا بمثله مددا) [الكهف: 109].
وأنّ كلام الله أحسن الكلام، وفضله على كلام الخلق كفضل الخالق على المخلوق.
ومن حكمة الله أنْ بعث الرسل وأنزل عليهم كُتُبَه؛ فأنزل التوراة والإنجيل والزبور وصحف إبراهيم وموسى وختمها بالقرآن العظيم؛ أحسنها نظمًا وأعظمها فضلا وأشرفها قدرا. والقرآن مصدِّقٌ لما بين يديه من الكتب ومهيمنًا عليها وناسخًا لها، ومؤتمنًا على ما كان فيها. وذكر القرآن والبشارة به موجود في زُبُر الأولين وكتبهم المأثورة عن الأنبياء الكرام.
والقرآن كلام رب العالمين؛ تكلم به بحرف وصوت مسموعَين، منه بدأ، وإلى الله يعود في آخر الزمان. سمعه خير الملائك؛ جبريل، ونزل به على خير الرسل، في أشرف البقاء، وفي خير شهر، وفي خير الليالي؛ ليلة القدر، لخير أمة، بأفضل اللغات وأجمعها.
كتاب لا يعدله كتاب. وهو مما امتنّ الله تعالى به على هذه الأمة. وشرَفٌ للنبي صلى الله عليه وسلم ولأمته (وإنه لَذِكرٌ لك ولقومك) [الزخرف: 44]، أي شرَفٌ لكم.
لا يصح إيمان العبد حتى يؤمن بالقرآن جملة وتفصيلا (يا أيها الذين ءامنوا بالله ورسوله والكتاب الذي نزّل على رسوله) [النساء: 136]، ولو أنزل القرآن على جبل لتصدع ذلا لله وطاعة، والمعرضُ عنه حَيٌّ بلا حياة.
حفظه الله قبل إنزاله في اللوح المحفوظ. وصانَه من الشياطين وقت نزوله. وتكفَّل بحفظه بعد نزوله. قدَّمه الله في الذكر على كثيرٍ مِن نِعَمه فقال: (الرحمن * علَّم القرآن).
كثُرَت أسماؤه، وتعددت أوصافه.
علَّم الله عباده القرآن ويسَّره لهم تلاوة وعملا وحفظًا؛ فيحفظه العربي والعجمي، والصغير والكبير والذكر والأنثى، والحر والعبد، والغني والفقير. جعله الله هدى للعالمين، فهو عامٌّ للبشرية كلّها كعموم رسالة نبينا صلى الله عليه وسلم؛ فلا تختص به أمةٌ دون أمة، يشبِه بعضُه بعضًا وتصدق آياتُه آياته. مستقيم لم يجعل الله له عوجًا، لا اختلاف فيه ولا تناقض. هو أفضل الحديث وأحسنه. وصفه الله تعالى بالعظمة فقال: (ولقد آتيناك سبعًا من المثاني والقرآن العظيم) [الحجر: 87].
وكتب الله له العلوَّ في ذاته وقدَرِه فقال: (وإنه في أم الكتاب لدينا لعليٌّ حكيم) [الزخرف: 4]. بيِّنٌ في لفظه ومعناه، وبيانٌ للأمور على جليَّتها. حكيمٌ؛ فيه ومنه الحكمة. كريمٌ عند الله؛ فيه من المكارم أعلاها، وبه يُكرَم العبد ويُعظَّم عند الله وعند خلقه. فيه هداية الخلق ومع الهداية فيه الرحمة. عِصمةٌ من الضلال لِمَن تمسك به. مجيدٌ بالغٌ في الشرف أعلاه. عزيزٌ لا يُجاريه في عِزِّه شيءٌ، ومَن دنا منه ناله العِزّ. عالٍ لا يُدانى، كثيرُ الخير والمنافع، ووجوه البركة فيه.
كتابُ الله نورٌ في الحياة لإبصار أمور الدنيا والآخرة، وبه تحيا الأرواح، فهو الحياة لمَن استجاب له. ومع حياة الأرواح به: فهو شفاء لأمراض الأبدان. بالقرآن تجتمع كلمة الأمة وتزول خلافاتهم. وبه فَصلُ الخلاف والنجاح. تحدى به الأولين والآخرين؛ إنسهم وجنَّهم. ما سمعَه عاقلٌ إلا شهِد أنه حق. خير الذكر وأفضلُه. هو تثبيتٌ للقلب عند الفتن والمصائب.
تلاوتُه تزيد الإيمان. آياتُه أبكَت العظَماء. وأمَر الله بإجارة المستجير مِن الكفار حتى يسمَع القرآن. حوى من العلوم أجمعَها ومن المعارف أنفعها، وأهله العارفون بمعانيه هم العلماء حقًّا. فيه مِن الأنباء أصدقها، ومِن البراهين والدلائل أقواها وأظهرُها، ومِن القصص أحسنها ومِن الحِكَم أبلغها، ومن البلاغة والفصاحة أجملها، والإعجاز في معناه أعظم وأكثر من الإعجاز في لفظه. كتاب الله شاملٌ في أحكامه عدلٌ في قضائه. حكيم في أمره ونهيه، عليه هيبةٌ وجلالٌ، وله قوَّة وتأثيرٌ وجمال. آية باهرة وعجزة ظاهرة، مَن عمل به أُجِر، ومَن حكم به عدَل، ومن تمسك به عُصم، ومن اتبعه رُحم.
مَن تلاه وعمِل به ونشَرَه في الآفاق عَزَّ وناله الأمنُ والرخاء. ومعلِّم القرآن ومتعلِّمه هم خيرُ الناس، قال صلى الله عليه وسلم: (خيركم مَن تعلَّم القرآن وعلَّمه)، رواه البخاري.
امتدح الله مَن تلاه وأثنى على العاملين به، ووعدهم بالوفاء والزيادة. هو التجارة الرابحة المضاعفة؛ مَن قرأ حرفًا منه فله حسنة، والحسنة بعشر أمثالها. وتعلُّمه خيرٌ مِن أموال الدنيا. والماهر بالقرآن مع السفرة الكرام البررة. مجالس القرآن ومظان تعلُّمه مواطن تنزّل السكينة والرحمة على المعلِّمين والمتعلِّمين. وباستماعه نيل الرحمات. التمسك به وتلاوته هو وصية النبي صلى الله عليه وسلم للأمة.
حاملُ القرآن مُكرم في حياته وبعد مماته، ففي الحياة يؤم القوم أقرأهم لكتاب الله، وبعد الوفاة يُقدم الأكثر أخذا للقرآن في اللحد. وأهل القرآن خيرُ جليس للمرأ.  وحجة لهله يوم الدين وشافعٌ مشفَّعٌ عند رب العالمين. وصاحب القرآن في أعلى درجات النعيم.

وبعد: أيها المسلمون! فالفرح بالقرآن وتعليمه من أرفع مقامات الإيمان. ولا غنى للأحد عن كتاب الله. وأسعد الناس أقربهم من كتاب الله. وهو أمان للمجتمع وبركة عليه، وفيه رضى رب العالمين. فحقيق بالمسم أن ينصر القرآن ويعتز به لينال أعلى الدرجات. بارك الله لي ولكم في القرآن العظيم ونفعني وإياكم بما فيه من الآيات والذكر الحكيم. 

ملحص خطبة يوم 7 من ربيع الأول 1437هـ بالمسحد النبوي في الوصية العظيمة التي وصى الرسول الكريم أمته


ملحص خطبة يوم 7 من ربيع الأول 1437هـ من المسحد النبوي في الوصية العظيمة التي وصى الرسول الكريم أمته
ألقى فضيلة الشيخ الدكتور حسين بن عبد العزيز آل الشيخ على منبر رسول الله صلى الله عليه وسلم خطبة الجمعة في هذا اليوم 07/ ربيع الأول / 1437هـ الموافق: 18/12/ 2015م، وتناول فيها الوصية العظيمة التي وصى بها رسول الله الله صلى الله عليه وسلم عبد الله بن عباس رضي الله عنهما (احفظ الله يحفظك، ...)، حيث بيَّن أنَّ حفظ الله المأمور به  هنا المراد به هو: حفظ حدود الله تعالى، والالتزام بحقوقه، والوقوف عند أوامره بالامتثال، وعند مناهيه بالاجتناب، وذلك بحفظ الرأس وما وعى من السمع والبصر واللسان، والبطن وما حوى، بحفظ الجوارح من الزلل، وضبط الشهوات ان تميل بصاحبها إلى الضلال، أو تجنح به عن مبادئ القيم وكريم الخلال، واستدل لذلك بمجموعة من النصوص الشرعية، منها قوله تعالى: ((هذا ما توعدون لكلّ أوّاب حفيظ * مَن خشي الرحمن بالغيب وجاء بقلبٍ منيبٍ)). وبقوله: وبقوله ((والحافظين فروجهم والحافظات والذاكرين الله كثيرًا والذاكرات أعد الله لهم مغفرة وأجرًا عظيمًا))، وبقول الرسول الكريم صلى الله عليه وسلم: "مَن يضمن لي ما بين لحييه وما بين رجليه أضمن له الجنة"، وبغير ذلك. وبيَّن الخطيب بأنّ العزّ بتحقيق هذه الوصية مضمون، والمجد في الدارين بتحقيق بنودها مرهون، وأنّ الأفراد بدون تحقيقها في ضياع، والمجتمعات في البعد عن مضامين الوصية إلى تشتت ودمار. وأنّ العمل بالوصية المتمحض في حفظ الله تعالى من الأفراد والمجتمعات هو الحل الوحيد لمشكلات الأمة.
ثم تكلم الخطيب عن حفظ الله تعالى لعبيده الذين حفظوه، ذلك أنّ الجزاء من جنس العمل، وأنّ حفظه لهم يشمل دينهم ودنياهم، ولهذا قال أهل العلم: حفظ الله للعبد يدخل فيه نوعان من الحفظ، الأول: حفظ الله لعبده في دينه وإيمانه، بحفظه من الشبهات المضلة، ومن الشهوات المحرمة، وذلك بالحيلولة بينه وبين ما يفسد عليه دينه. النوع الثاني من الحفظ: حفظ الله للعبد في مصالح دنياه، كحفظه في بدنه، وولده وأهله وماله، ((له معقبات من بين يديه ومن خلفه يحفظونه من أمر الله)). ومما يدخل في هذا: حفظ الله للعبد الصالح في ذريته بعد موته، كما في قصة اليتيمين من سورة الكهف اللذين حُفظا في كنزهما بإقامة الجدار لصلاح أبيهما رحمة من الله ((وكان أبوهما صالحا)).
وفي ضمن الوصية والخطبة بيَّن الخطيب أنّ الأمة الإسلامية على مستوى الأفراد والمجتمعات، وبمختلف المسئوليات والمكانة متى ما حفظت دين الله (فحققت الإيمان الصادق بالله، واستسلمت لأمره في كل شأن، وتخلصت من أهواء النفوس، وشهوات القلوب، وكانت أحوالها السياسية والاقتصادية والاجتماعية والأمنية وغيرها على مقتضى منهج الله وشريعته، وعلى سنة رسول الله صلى الله عليه وسلم، ومتى جعلت الإسلام الصافي منهاجًا كاملا لحياتها في كل أطوارها، وفي جميع علاقاتها، وارتباطاتها، وفي كل حركاتها: حينئذٍ يتحقق لها حفظ الله لها من المكاره والمشاق والأزمات والمحن، ويحصل لها الأمن والاستقرار والعزة والانتصار.

وتساءل الخطيب حفظه الله تعالى بأنه كيف يحصل الوعد بالحفظ والعزة والمنعة لأمة نبذت كتاب الله وسنة رسوله الكريم، فلم تتخذ الشريعة الإسلامية منهاج حياة واحتكام، بل اعتاضت بالقوانين الوضعية الوضيعة، أم كيف يحصل حفظ لأمة توجهت إلى القبور ترجوها من دون الله كما هو الحال في مواطن كثيرة لا تخفى من بلدان المسلمين، وكيف... وكيف... فاللهم إنا نسألك الإعانة على حفظ دينك، وأصلح أوضاعنا وأوضاع المسلمين، واحفظنا برحمتك، يا رب العالمين.      

2015/12/17

HUDUBAR JUMA'A DAGA MASALLACIN ANNABI saw 07 Rabiyul Auwal 1437h, daidai da 18 Disamba 2015m, ta Assheikh Husain Alus-sheikh








HUXUBAR MASALLACIN ANNABI (صلى الله عليه وسلم)
JUMA'A, 07/RABI'UL  AUWAL/1437h
Daidai da 18 /DISAMBA/2015m



LIMAMI MAI HUXUBA
SHEHIN MALAMI HUSAIN XAN ABDUL'AZIZ ALUSH SHEIKH







TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
بسم الله الرحمن الرحيم
Godiya ta tabbata ga Allah; Majivincin mumunai, Wanda yake tsare masu bin dokokinSa, Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; Shi kaxai yake ba shi da abokin tarayya; Abun bautar na-farko da na-qarshe.
Kuma ina shaidawa lallai annabinmu Muhammadu bawansa ne kuma manzonsa; Zavavve Amintacce.
Ya Allah ka yi salati a gare shi da sallama, da albarka, Shi; da iyalansa da sahabbansa gabaxaya.
Bayan haka:

Ya ku Musulmai!!
Ina yin wasiyayya a gare ku da Ni kaina, da kiyaye dokokin Allah (taqawa), saboda bin dokokinSa shine tsira, kuma yin xa'a a gare shi shine rabauta.

Ya ku Musulmai!!
Cikin tarin matsalolin da suka addabi al'ummarmu ta Musulmai masu yawa, a cikin vangarorin siyasa, da tattalin arziqi, da zamantakewa, da aminci ko zaman lafiya, da wassu vangarorin. Da kuma abinda al'ummar take rayuwa a cikinsa na halin rauni da rarrabuwa, da kuma xanxanar nau'ukan qasqanci da wulaqanci, da shan bonen rarrabuwar kai da qungiyanci.  To lallai Ma'abuta hankula suna jira ko fatan ganin lokacin da za a tsamar da wannan al'ummar daga munanan abubuwan da suka addabe ta.
Kuma lallai Masana sun faxi albarkacin bakinsu, Shugabanni suma sun kawo irin mafitar da suke gani, Marubuta suma sun ambaci abinda suka yi nazari. Maganganu sun yi yawa kan menene sabbuban da suka janyo hakan, kuma ra'ayoyi sun banbanta kan mafita, da kuma hanyoyin da za a warware matsalolin.
Saidai kuma, Lokaci yayi ga al'ummar Musulmai gabaxayanta; qasashensu da xaixaikunsu, Shugabanni da waxanda ake shugabanta, Su ga haqiqanin waxannan matsaloli, sannan su fitar da nagartattun hanyoyin da za a bi don magance su, daga abinda ya tabbata daga addininsu, da kuma ginshiqansa da ake dogara a kansu.
            Kuma lallai al'ummar Musulmai ba za su tava samun nagartattun magani ga cutukansu ba, da kuma mafita daga halin da suke ciki da kuma mushkilolinsu ba, Sai kawai ta hanyar kyakkyawar fahimta ga LITTAFIN ALLAH DA SUNNAR ANNABINMU MUHAMMADU (صلى الله عليه وسلم).

            'Yan'uwan Musulunci!
            (A yanzu) za mu saurari wasiyya ce mai girma wacce Malamin duniya kuma shugaban halitta ya aiwatar da ita a gare mu; wato Annabinmu Muhammadu (صلى الله عليه وسلم), a lokacin da ya ke faxakar da al'ummarsa, kuma yake bata wasiqar da za ta tabbata har abada; wacce kuma za ta gyara wa al'umma rayuwarta idan suka bi abinda ke cikinta, sannan xaixaikunta su rabauta, su kuma samu bunqasa idan suka yi aiki da ita.
Wasiqa ce, da ya zama wajibi a ko-da-yaushe ta zama, a gaban idanunmu, Yin aiki da ita kuma ya game dukkan aiyukanmu, ta hanyar faxakar da mu cikin kowani motsawarmu, da yin gyara cikin nufinmu ko qudurinmu, da aiyukan da muka fiskanta.
Wasiqa ce, da ba tana dubi ko rinjayar da maslahar wassu mutane ba, ko kuma raya qabilanci, ko kuma warware matsalar yau (kawai) ba.
Wasiqa ce da ta fito daga wanda baya yin Magana daga son zuciya, kuma baya cewa komai sai daga wahayin da ake aiko masa.
Wasiqar da Annabi Muhammadu (s.a.w) yazo da ita, kuma wasiyya mai haske, Wacce za ta bunqasa Musulmai zuwa ga rayuwa maxaukakiya, wacce ta cika da alkhairi da rinjayen buwaya, da aikin nagarta, da samun qarfi,
"Ya ku waxanda suka yi imani! ku amsa wa Allah, da kuma Manzo, idan ya kiraye ku zuwa ga abinda zai raya ku" [Anfal: 24].
Irin Rayarwa gamammiya, ga xaixaikun Mutane da kuma jama'a, da kuma rayuka da kaya masu qima wanda aka mallaka. Irin rayuwar da ake gina ta akan QARFIN IMANI, wanda babu makawa sai da shi, gabanin a iya fiskantar matsaloli. Rayuwar da take nufin: Bunqasa; da faffaxar ma'anarta, da kuma dukkan surorinta, wacce za ta tattara wa al'ummar Musulmai samun walwala, da rayuwa cikin aminci da tsaro, da alherori da bunqasa, da samun xaukaka a kowani fage daga cikin fagagen rayuwa.

            Ya ku Musulmai!!
            Lallai samun buwaya Na nan ne kawai cikin aiki da wannan wasiqar, kuma lallai samun girma a duniya da lahira idan aka yi aiki da abinda ta qunsa abu ne da ake da tabbacinsa, Allah mabuwayi da xaukaka yana cewa:
"Kuma lallai haqiqa mun saukar zuwa gare ku, da wani littafi, a cikinsa akwai xaukakarku" [Anbiya'i: 10]. Kuma Allah yana cewa:
"Kuma wanda ya yi taqawa, kuma ya gyara aikinsa, To, babu tsoro akansu, kuma ba su yin baqin-ciki" [A'araf: 35].
            Xaixaikun Mutane, Idan har ba su yi aiki da wannan wasiyar ba, suna cikin tozarta. Kuma suma al'ummomi idan suka yi nisa da abubuwan da ta qunsa za su wargaje; su rushe.
            Wasiqa ce da take qulle Musulmi da asalinsa, tare da sadar da shi da zamaninsa. Ta kuma tattara masa bin abinda shari'a ta zo masa da shi, da dacewa da samun abinda zamani ya hukunta. Wasiqa ce wanda yin aiki da ita shine hanya guda xaya kwara da za a magance  matsalolin da suke fiskantar al'ummar Musulmai, waxanda kuma suke fiskantar ginshiqanta da abinda suke girmamawa da abubuwan da suke kevance ta, don su lalata. Umar Alfaruq (رضي الله عنه) yace:
"Lallai kawai kun rigayi Mutane ne, da taimakon wannan addinin".

            Sai mu saurara –Allah ya kare ku-
            Don jin wannan wasiyyar mai girma, kana kuma wasiqa mai dawwama, Ji irin na amsawa da aiki, da kuma bi da miqa wuya, Abdullahi xan Abbas (رضي الله عنهما) yace:
Na kasance a bayan Manzon Allah (S.A.W) wata rana sai yace da ni, “Ya kai yaro! Zan sanar da kai wasu kalmomi: Ka kiyaye Allah, sai ya kiyaye ka; ka kiyaye Allah za ka same shi a gaba gare ka (yana yi maka jagoranci); idan zaka roqa to ka roqi Allah; idan zaka nemi taimako ka nemi taimakon Allah. Ka sani, da al’umma za su taru domin su amfane ka da wani abu, ba za su iya amfanar da kai komai ba , sai da abinda Allah ya rubuta maka. Idan kuma da al’umma za su taru domin su cuce ka da wani abu, ba za su cuce ka ba, sai da abinda Allah ya rubuta maka. An xauke alkaluma, takardun kuma sun bushe”. Tirmiziy [2516] ya ruwaito shi, yace hadisi ne mai kyau ingantacce.
A riwayar wanin Tirmiziy kuma: “
Ka kiyaye dokar Allah, zaka samu Ubangiji a gabanka, ka nemi sanin Allah a lokacin da ka ke cikin yalwa, zai san da kai a lokacin da kake cikin tsanani. Ka sani! Duk abinda ya kuskure maka, to bai kasance zai same ka ba. Duk kuma abinda ya same ka bai kasance zai kuskure maka ba. Ka sani, lallai cin nasara yana tare da haquri, yayewa kuma tana tare da baqin ciki, kuma lallai a tare da tsanani akwai sauki”.
           
Ma'abuta ilimi suka ce:
Lallai wannan hadisin yana qunsar wasiyyoyi masu girma, da kuma qa'idodi daga cikin muhimman lamuran addini, Har wassunsu suka ce:
Na yi tunanin wannan hadisin sai ma'anarsa ta sanya ni cikin ximuwa, har na yi kusan Na kixime, Saidai abin haushin shine: Yadda Mutane suka jahilci wannan hadisin, kana suke da qarancin fahimta, ga ma'anarsa.

Ya ku Musulmai!!
KIYAYE ALLAH (احفظ الله) da ake nufi a cikin wannan hadisin shine:
KIYAYE DOKOKINSA, DA AIKIN BASHI HAQQOQINSA, DA TSAYUWA GA UMURNINSA DA BINSU, WAJEN HANINSA KUMA DA NISANTA, Allah mabuwayi da xaukaka yana cewa:
"Wannan shine abinda ake yin alkawari a gare ku ga dukkan mai yawan komawa ga Allah, mai kiyaye dokokinsa   *   Wanda yaji tsoron  Mai rahama a fake, kuma ya zo da wata zuciya mai tawakkali" [qaf: 32-33].
            KIYAYEWA NE, da ya haxa da kiyaye KAI da abinda ya tattara (NA HARSHE DA JI DA GANI), da kiyaye CIKI da abinda ya qunsa (NA FARJI DA QAFA…), Imam Ahmad da Attirmiziy sun fitar daga hadisin Abdullahi xan Mas'ud (رضي الله عنه), daga Annabi (صلى الله عليه وسلم), yace:
"JIN KUNYAR ALLAH IYAKAR JIN KUNYARSA shine: Ka kiyaye KAI da abinda ya tattara, da kuma CIKI da abinda ya qunsa".
            KIYAYEWA NE da yake hana gavvai  zamewa da aikata laifuka, Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Duk wanda ya kiyaye min abin da ke tsakanin havansa biyu, da abinda ke tsakanin qafofinsa Na lamunce masa shiga aljanna", Bukhariy ya ruwaito shi.
                KIYAYEWA NE da yake kare sha'awa daga bauxewa zuwa ga vata daga ma'abucinta, ko ta karkace da su daga kyawawan halayya abun yabo zuwa ga kishiyan haka, Allah mabuwayi da xaukaka yana cewa:
"Da masu kiyaye farjojinsu maza da mata masu kiyaye farjojinsu, da maza masu ambaton Allah dayawa, da kuma mata, Allah ya musu tanadin gafara da wani lada mai girma" [Ahzab: 35].

            Ya ku taron Muminai!!
            Yana daga qa'idodin addini Lallai sakamako, ya kan zama daga jinsin aiki; Don haka; Duk wanda ya samar da KIYAYE ALLAH da irin ma'anarsa da ta gabata, To, sai ya samu KIYAYEWAR ALLAH DA KULAWARSA DA BADA KARIYARSA; Kiyayewar da ta haxa da vangaren addininsa da duniyarsa, ya kuma tabbatar wa bawa maslaha da dukkan nau'ukanta, da kuma tunkuxe masa cutuka da dukkan kalolinsu.

            Ma'abuta ilimi sun ce: KIYAYEWAN DA ALLAH KE YI WA BAWANSA, Nau'uka biyu na kiyayewa ne ke shiga qarqashinsa:
            NA FARKONSU: Kiyayewan da Allah ke yi wa bawa, cikin addininsa, da imaninsa; ta hanyar kiyaye shi daga faxawa cikin cutukan SHUBUHOHI (BIDI'OI) masu vatar da Mutane, da kuma SHA'AWOWI na haram; Sai ya sanya masa abinda zai katange shi daga faxawa cikin abubuwan da za su lalata masa addininsa, Allah mabuwayi da xaukaka yana cewa:
"Kamar haka dai, Domin mu kawar da mummunan aiki da alfasha a gare shi, lallai ne shi ya kasance daga cikin bayinmu zavavvu" [Yusuf: 24].
            NAU'I NA BIYU: Ya kiyaye shi cikin maslahohinsa na duniya, kamar Allah ya kiyaye masa jikinsa, da 'ya'yansa, da iyalansa, da dukiyoyinsa, Allah mabuwayi da xaukaka yana cewa:
"(Mutum) yana da Mala'iku masu maye wa juna a gaba gare shi, da baya gare shi, suna tsare shi, da umurnin Allah" [Ra'ad: 11].
Abdullahi xan Abbas  (رضي الله عنهما) yace:
"Mala'iku suna kiyaye shi, da umurnin Allah, Saidai Idan qaddarar da aka qaddara masa ta zo, sai su qale shi".
Alhafiz Ibnu-rajab –Allah yayi masa rahama- yace:
"Daga abin mamakin kiyayewar Allah ga wanda Allah zai kiyaye, shi ne: Allah ya sanya dabbobin da a xabi'arsu cutarwa suke yi, su kiyaye bawa daga wani abinda zai cutar da shi, kamar yadda hakan ya gudana ga Safinatu; 'yantaccen bawan Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم), a lokacin da jirgin kwale-kwale ya karye da shi, ya fita zuwa ga wani tsibiri, sai ya ga wani zaki, sai zakin yayi ta tafiya tare da shi, har sai da ya nuna masa hanya", Ta qare.
            Kuma lallai Annabi (صلى الله عليه وسلم) ya qarfafa wannan ma'anar, a cikin wannan wasiyar, a inda yace: Ka kiyaye dokar Allah, zaka samu Ubangiji a gabanka"; Don haka, duk wanda ya kiyaye dokokin Allah, ya kuma lura da haqqoqinsa Sai Allah ya kewaye shi da tsarewarsa, ya kuma yi baiwa a gare shi da datarwarsa da daidaitawarsa, Ya dawo masa da qarfafarsa da taimakonsa, Allah yana cewa:
"Lallai Allah, yana tare da masu taqawa, waxanda suke su masu kyautatawa ne" [Nahli: 128].
Qatadah (رضي الله عنه) yace: "Wanda ya yi taqawar Allah, Allah ya kan kasance tare da shi, Duk kuma wanda Allah ya kasance tare da shi To yana tare da jama'ar da ba a rinjayarta, da kuma mai-gadin da baya barci, da mai shiryarwar da baya bacewa".
Wani daga cikin magabatan kwarai ya rubuta wasiqa zuwa ga 'xan'uwansa; Ya ce:
"Bayan haka: In har Allah ya kasance a tare da kai, To wa zaka ji tsoro? Idan kuma ya kasance akanka To wa za ka yi fata?".

            'Yan'uwan Musulunci!!  
            Yana daga abinda wannan NAU'IN ya qunsa: Kasancewar Allah ya kan tsare, ko ya kare zuriyar salihin bawa, a bayan mutuwarsa, kamar yadda Allah mabuwayi da xaukaka yake cewa:
"Kuma Ubansu ya kasance salihin mutum" [Kahf: 82]. Maluma suka ce: Waxannan marayun guda biyu an basu tsarewa da kariya ne, saboda kasancewar ubansu salihi.
Kamar yadda Allah mabuwayi da xaukaka yake cewa:
"Kuma waxanda suke, da sun bar zurriya masu rauni a bayansu, za su riqa tsorace musu, To su kiyayi Allah (dangane da marayun da suke hannunsu), kuma su riqa faxar Magana madaidaiciya" [Nisa'i: 9].

            Kuma duk wanda ya KIYAYE ALLAH (DA DOKOKINSA) A CIKIN QURUCIYARSA DA QARFINSA Sai Allah ya tsare shi a lokacin tsufansa da raunin qarfinsa, kuma ya jiyar da shi daxi; da jinsa, da ganinsa, da wayonsa da qarfinsa. Wani daga cikin magabatan kwarai ya qetare shekaru xari, alhalin yana cikin qarfinsa da hankalinsa, Sai wata rana ya kai cafka ga wani abu da qarfi, Sai aka yi masa Magana akan haka, Sai ya ce:
"Waxannan gavvai ne, da muka tsare su daga savon Allah a lokacin quruciya, Sai Allah ya kiyaye mana su, a lokacin tsufanmu".

            Jama'ar Musulmai!!
            Lallai wannan al'ummar; xaixaikunta da jama'ointa, da kuma mabanbantan matsayinsu, da irin nauyin da ke hawa wuyansu, Duk lokacin da suka kiyaye addinin Allah; suka yi Imani na gaskiya da Allah, suka miqa wuya ga lamarinSa cikin kowani sha'ani, suka nemi kuvuta daga bin son rayuka, da sha'awowin zukata, kuma halinsu na siyasa da tattalin arziqi da zamantakewa da wassunsu suka kasance kamar yadda tsarin Allah, da sunnar Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) suka hukunta, Duk lokacin da al'ummar ta sanya, Musulunci, tatacce, ya zama cikakken tsarin rayuwarta, a cikin dukkan matakai, da kuma cikin dukkan alaqoqin da za ta yi, da dukkan motsawanta da shirunta, To, a lokacin ne za su samu KIYAYEWAR ALLAH a gare su, dangane da dukkan abin qi, da wahalhalu, da fitintinu da matsalolin da al'ummar suke fama da su, Kuma a lokacin ne, za su samu AMINCI da ZAMAN LAFIYA, da BUWAYA, da TAIMAKO, Allah mabuwayi da xaukaka yana cewa:
"Waxanda suka yi imani, kuma basu gauraya imaninsu da zalunci ba, waxannan suna da aminci, kuma sune shiryayyu" [An'am: 82].
            Kuma lallai al'umma a duk lokacin da IMANI DA ALLAH, da NEMAN KOYI DA MANZONSA (صلى الله عليه وسلم) ya game dukkan rayuwarsu, kana hakan ya jagoranci dukkan abinda zasu fiskanta, da duk motsawansu To, sai AMINCI da dukkan nau'ukansa ya kasance a gare su; kamar amintuwa daga abokan gaba, da abubuwa masu hatsari, da aminci daga abubuwan tsoro da cutuka, da aminci cikin shugabanci da siyasa, da aminci cikin tattalin arziqi, da aminci cikin zamantakewa,  Kuma duk lokacin da Musulmai gabaxayansu suka tsayu wajen bin addininsu da karantarwar Musuluncinsu, suka kuma nisanci son rayuka da bin sha'awowi, kuma suka yi aiki tuquru da gaskiya wa Musulunci, tare da yin aiki da sabbuban samun xaukaka da bunqasa da cin nasara, da kuma yin tanadi wa maqiya,   To, a nan ne, Allah zai basu kafuwa a bayan qasa, ya kuma qarfafa su, ya bada buwaya ga kalmarsu, ya kuma sanya tsoronsu a cikin zukatan maqiyansu, tare da game su, da basu alheri, da adalci, da zaman lafiya,
"Allah ya yi alkawari ga waxanda suka yi imani, daga cikinku, kuma suka aikata aiyuka kyawawa, lallai zai shugabantar da su a cikin qasa kamar yadda ya shugabantar da waxanda suke daga gabaninsu, kuma lallai ne zai tabbatar musu da addininsu wanda ya yarda musu, kuma lallai ne, zai musanya musu, daga bayan tsoro, da wani aminci, suna bauta mini basa haxa ni da komai. Kuma wanda ya kafirta a bayan wannan, lallai waxancan, sune fasiqai" [Nur: 54-55 ].

            Taron jama'ar Muminai,,,,,
            Lallai wannan al'ummar duk lokacin da bala'i ya sauka a cikinta, kuma ta xanxani jarabawar rayuwa, Ta samu tsoro sai ta nemi aminci, ko ta qasqanta Sai ta nemi hanyar samun buwaya, ko ta ci-baya Sai ta nemi fatan samun khilafanci a bayan qasa da zaman lafiya, Saidai ba za ta tava samun daman hakan ba, kuma al'umma ba za ta tava samun abubuwan da take fatan samunsu ba matuqar basu tsayu wajen aiki da sharaxin da Allah ya kafa ba; na tsayuwa da yin xa'a wa Allah da Manzonsa (صلى الله عليه وسلم), da kuma yarda cikakkiya, da shari'ar Allah, da kuma aiki da wannan tsarin na Musulunci abin yarda, To, kuma a lokacin ne varna za ta kau, da koma-baya, sannan tsoro da firgici da rashin aminci su kau daga gare su, kuma a wannan lokacin babu wani qarfi daga cikin masu qarfin duniya za su tsaya akan hanyarsu, Allah mabuwayi da xaukaka yana cewa:
"To, idan wata shiriya daga gare Ni ta zo muku, to, wanda ya bi shiryarwarta, to baya vacewa, kuma baya wahala   *   Kuma duk wanda ya bijire daga ambatona (alqur'ani) to, lallai ne rayuwa mai qunci ta tabbata a gare shi, kuma za mu tayar da shi a ranar qiyama yana makaho" [Xaha: 123-124].
Kuma Allah (تعالى) yace:
"Duk wanda ya bi shiryarwa ta to babu tsoro akansu kuma ba za su yi baqin ciki ba" [Baqara: 38].

            'Yan'uwan Musulunci!!
            Babu wata al'umma Musulmai  a tsawon tarihi, wanda za su sava wa wannan tsarin (na Musulunci), face ta ci baya; ta koma qarshen tawaga, sai ta qasqanta, kana a kore ta daga jagoranci, sai kuma tsoro ya mamaye ta, Maqiya kuma face sun yi mata xauki-xaxxaya, kamar yadda Allah mabuwayi da xaukaka yake cewa:
"Shin, a lokacin da wata musiba ta same ku, alhalin kuwa kun samar da irinta guda biyu, Sai kuka ce: Daga ina wannan yake? Ka ce, Wannan daga rayukanku yake?"[Ali-imrana: 165].
Ya tabbata daga Annabi (صلى الله عليه وسلم), a matsayinsa na Mai rahama da Tausayi ga al'ummarsa, Yace:
"Idan kuka yi kasuwanci irin na iynah (sayar da abu da bashi zuwa wani lokaci, sannan ya sake sayansa da kuxi a hannu, qasa da na farkon), kuma kuka kama jelar shanu (kiyo), kuma kuka yarda da noma, sai kuka bar yin jihadi, to Allah sai ya xora muku wani irin qasqanci; ba zai cire shi ba har sai kun koma zuwa ga addininku".

            Al'ummar Musulunci, a kowani wuri !! Mu sani, Lallai alqawarin Allah a tsaye yake, duk yadda aka samu canjin zamani ko na hali; Duk lokacin da sharaxin da aka ambata ya tsayu; ya tabbatu; Don haka:
Duk wanda ya ke son tabbatuwan wannan alqawarin sai ya yi aiki da sharaxin; "Kuma wane ne, mafi cikawa ga alqawarinsa fiye da Allah? (Babu!)" [Tauba: 111].

            Wannan ya sanya, Magabatan kwarai daga cikin sahabbai da waxanda suka zo, a bayansu suka tafi akan wannan tsarin (na Musulunci) suna masu samun amintuwa da Allah, da dogaro a gare shi, da qarfafa imaninsu da shi, da tabbatuwa cikin azama, da yin haquri a lokutan wuya ko tsanani, da cikakken bi, ga mafi alherin jagora; Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم), tare da yin jihadi, da qoqartawa, da aikata aiyukan alkhairi ba tare da qaqqautawa ko yankewa ba, Kuma a lokacin ne, Allah ya tsayar da ginin wannan addinin da Su, kuma daular Musulunci mai qarfi ta kafu a sasanin duniya, Wannan kuma saboda, Sun auna DUNIYA da ma'auninta na haqiqa, kuma ba su karkata zuwa gare ta ba, kuma sun san cewa ita (duniya) qasqantacciya ce, mai saurin gushewa; sai ba su yarda suka yaudari kansu da ita ba, Sun kuma SAN LAHIRA; Sai suka bata matsayin da ta cancanta, kuma suka sanya ta, gaba ga idanuwansu; Don samun tabbatuwa a cikin ni'imominta suka kasance suke yin aiyuka, kuma akan haka suke kwallafa kwaxayinsu, Sai aiyuka masu tsabar wahala suka yi sauqi a gare su, saboda haka.

            Ibnu-Kasir –Allah yayi masa rahama- ya ambata, cikin abubuwan da suka auku a shekarar hijira ta xari huxu da sittin da uku (463h) cewa:
((Mai mulkar kafiran Rumawa sai ya fiskanto cikin rundunonin da ba za su qirgu ba; saboda yawa, misalin duwatsu, da tanadi mai yawa, da kuma jam'i mai tayar da hankali, Yana kuma daga cikin niyyarsa; Wai ya tunvuke Musulunci, da ma'abutansu, Sai jagoran Musulmai ya haxu da shi, a cikin rundunar da bata wuce Mutane dubu ashirin ba, ya kuma ji tsoron yawan mushirkai, Sai faqihin Malami Abu-Nasrin; Muhammadu xan Abdulmalik mutumin garin Bukhara ya bashi shawarin cewa lokacin gwabzawa a yaqin ya kasance ranar juma'a ne bayan rana ta yi zawali; a lokacin da masu huxuba suke yin addu'oi ga masu jihadi, Kuma a lokacin da vangarorin guda biyu suka fiskanci juna don fara yaqin sai shugaban Musulmai ya sauka daga dokinsa, ya faxi ya yi sujjada wa Allah mabuwayi da xaukaka, ya kuma roqe shi maxaukaki, ya nemi nasararSa, Sai Allah ya saukar da nasararSa ga Musulmai, ya kuma mallaka musu kafaxun Mushirkai, sai hakan ya kasance nasara ce mai qarfi mai girma)). Maganarsa ta qare.
            Shi kuma halin da Musulmai suke cikinsa a yau, yana buqatar sake nazari, da kuma yin gyara na gaskiya.  
            Taron Musulmai!!
            Ta yaya alkawarin tsarewa da kiyayewa zai tabbata a yau? Ga Mutanen da suka kawar da kansu daga hukuntar da wahayin alqur'ani da Sunnah, sai suka gudu zuwa ga tsare-tsaren da suka sanya da kansu da kuma kundayen da Mutane suka samar? kamar yadda hakan shine halin da al'umma ta kasance a cikinsa tun fiye da shekaru xari. Kuma dayawa daga cikin qasashensu basu gushe ba a cikin haka, har zuwa yau.
            Kuma ta yaya, nasara da buwaya da gyara zai kasance, ga Mutanen da fiskantar wanin Allah ya yawaita a cikinsu, kamar yadda hakan shine halin da ake ciki a wajen wassu qaburbura, a wurare dayawa waxanda ba voyayyu ba ne,  daga garurrukan Musulmai!
            Kuma ta yaya wassu Mutane za su rabauta; alhalin tsarinsu na tattalin arziqi, ya ginu akan riba da aka haramta, da kuma sauran mu'amalolin da suka sava wa littafin Allah, da sunnar ManzonSa Muhammadu (صلى الله عليه وسلم)? Sai kuka wayi gari suna koyi da kafiran gabacin duniya ('yan gurguzu), ko na yamma ('yan jari hujja).
            Kuma ta yaya wassu Mutane za su rabauta? Kuma ta yaya al'umma zata tsira, alhalin munanan abubuwa sun yaxu a cikinta, da abubuwan kyama, kamar yadda haka halin yake a wassu daga cikin garurrukan Musulmai a yau!
            Kuma ta yaya wassu Mutane za su xaukaka, alhalin bada rashawa da karvarta sun yaxu a cikinsu? Sannan kuma qarya da fajirci da algus da yaudara sun yaqe su, Sannan, a cikin dayawa daga cikin mu'amalolinsu an rasa gaskiya da amana, da dukkan nau'ointa?
            Kuma ta yaya halayen dayawa daga cikin Musulmai za su gyaru, alhalin kuma a wajjen wassu daga cikin 'ya'yan Musulmai an rasa tutar soyayya don Allah, da kuma qiyayya don Shi, Sai duniya (da kuxi) suka wayi gari su suke hukunta, soyayya, da barranta (ko qiyayya).
Ya Allah! Ka gyara yanayin Musulmai!
Ya Allah! Ka gyara yanayinmu da yanayin Musulmai!
Ya Allah! Ka gyara yanayinmu da yanayin Musulmai! Ya mafi rahamar masu jin qai!
            Allah yayi albarka wa NI da KU, cikin alqur'ani, kuma ya amfanar da MU da abinda ke cikinsa na ayoyi da bayani. Ina faxar wannan maganar, kuma ina neman gafarar Allah wa NI da KU da SAURAN Musulmai, daga kowani zunubi, ku nemi gafararsa; lallai shi mai yawan gafara ne mai rahama! …

 
HUXUBA TA BIYU:
            Gidiya ta tabbata ga Allah shi kaxai, kuma ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai; bashi da abokin tarayya. Kuma ina shaidawa lallai annabi Muhammadu bawansa ne kuma manzonsa. Ya Allah ka yi salati da sallama a gare shi, da iyalansa da sahabbansa gabaxaya.
            Bayan haka:
           
Ya ku Musulmai!!
            Duk wanda ya kiyaye dokokin Allah; Sai Allah ya lare shi, kuma sai ya sanya masa yayewa daga kowani baqin ciki, da kuma mafita daga kowani qunci, Sannan ya azurta shi ta inda baya tsammani .

Ya ku taron Muminai!!
            Lallai kwanaki da lokatai suna ta wucewa alhalin 'yan'uwanmu a qasar Falasxinu suna fama da yanayi mai tsoratarwa na zubar da jininsu da ake yi, da sassara su (gunduwa-gunduwa), da korarsu da kakkashe su, Wucewan kwanaki zai yi wuya ya goge hakan, ko kuma kwakwale su manta su, Tsoratarwa mummuna, daga Yahudawan kama-wuri zauna (Sahayinah); masu kwace gidaje, Wanda masu kashe Mutane da zubar da jini suke zartar da shi akansu; da dukkan nau'ukansa da shakalinsa.
            Ya kai mai gani! A ina wai, masu sanya doka suke na duniya, a lokacin da suke ganin wannan sharrin yana tunbatsa, da wannan zaluncin da yake ta girma?!
Kwaxayin kwace abin wani, wanda ba shi da iyaka, ko ma'auni, Daga yahudawan Sahayina masu kwace!
           
            To, Duniya gabaxayanta ta sani, lallai mafita kawai tana nan ne, cikin bayar da haqqoqi ga ma'abutansu, da kuma yaxa adalci na haqiqa a tsakanin Mutane gabaxayansu (ba tare da wariya ba), tare da kiyaye karamar Mutum da matsayinsa wanda Musulunci ya zo da shi.    

            Ya ku 'Ya'yan al'ummar annabi Muhammadu (صلى الله عليه وسلم) wannan lamarin yana da hatsari mai girma, kuma tambaya a gaban Allah tana da girma dangane da taimakon lamuran Musulmai, kuma wajibi ne mu tsaya daram tare da 'yan'uwanmu Muminai da suke qasar falasxinu ko waninta daga cikin wuraren Musulmai,  Ina haxa ku da Allah, ina haxa ku da Allah, wajen sauke wannan wajibin; kowani Mutum gwargwadon ikonsa, cikin abinda zai iya, Ku aika musu dukiya, da gamsuwar zuci, Ku fiskanci Allah mabuwayi da xaukaka da yin managartan addu'oi a gare su, a kowani lokaci da zamani, ALLAH SHINE WANDA AKE NEMAN TAIMAKONSA, ZUWA GARE SHI AKE YIN KOKE, KUMA AKANSA AKE DOGARA, KUMA LALLAI SHI, YA ISAR MANA, MADALLA DA SHI, ABIN DOGARO.

Sannan ku sani, Lallai mafi tsarkin abinda rayuwarmu za ta tsayu akansa shine: Shagaltuwa da yin salati da sallama ga Annabi mai karamci.
Ya Allah!  Ka yi salati da sallama da albarka ga bawanka kuma manzonka; annabinmu Muhammadu.
Ya Allah! Ka yarda da khalifofi shiryayyu, kuma jagorori masu shiryarwa; Abubakar da Umar, da Usman, da Aliyu.
Ya Allah! Ka gyara halinmu da halin Musulmai.
Ya Allah! Ka yaye baqin ciki, ka kore ababen baqanta rai.
Ya Allah! Ka tseratar da bayinka Musulmai daga kowani ibtila'i da fitina.
Ya Allah! Ka yi maganin maqiyan Musulmai; Lallai su, basu gagare ka ba, Ya Mai girma!
Ya Allah! Ka kiyaye 'yan'uwanmu Musulmai a kowani wuri, Ya Allah ka kasance mai taimako a gare su; Ya Mabuwayi ya Mai matsanancin qarfi.
Ya Allah! Ka datar da Mai hidiman Masallatan harami biyu zuwa ga abinda kake so, kuma ka yarda da shi, Ya Allah ka taimaki addininka da shi, kuma ka xaukaka kalmar Musulmai da shi.
Ya Allah! Ka gafarta wa Musulmai maza da Musulamai mata; rayayyu daga cikinsu da kuma matattu.

Ya Allah! Ka bamu mai kyau a Duniya, a Lahira itama mai kyau, kuma ka kare mu daga azabar Wuta.

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...