2015/11/05

HUDUBAR MASALLACIN ANNABI saw Ta Sheikh Assubaitiy 24 Almuharram 1437hijira daidai 06 11 2015m








HUXUBAR MASALLACIN ANNABI (صلى الله عليه وسلم)
JUMA'A,24/ALMUHARRAM/1437H






LIMAMI MAI HUXUBA
SHEHIN MALAMI DR. ABDULBARIY XAN AWWADH AS-SUBAITIY







TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
بسم الله الرحمن الرحيم
Godiya ta tabbata ga Allah, wanda ya halitta Mutum, ya kuma ilmantar da shi bayani, Ina yin yabo a gare shi, tsarki ya tabbata a gare shi- kuma ina gode masa; akan ni'imar shiriya da Imani,
Kuma ina shaidawababu abinbautawa da gaskiya sai Allah; shi kaxai yake bashi da abokin tarayya, Mai karimci Mai girma  Mai yawan baiwa.
Kuma ina shaidawa lallai shugabanmu kuma annabinmu Muhammadu bawan Allah ne kuma Manzonsa, Ma'abocin falala da kyautatawa.
Allah yayi daxin salati da sallama a gare shi, da iyalansa da sahabbansa, duk lokacin da rana da wata suka yi canjin aiki.

Bayan haka:
            Ina yi muku wasici da ni kaina da kiyaye dokokin Allah; Allah yana cewa:
"Ya ku waxanda suka yi imani ku kiyaye dokokin Allah iyakar kiyayewa, kuma kada ku mutu face kuna Musulmai" [Ali-imrana: 102].

Lallai haqiqa Allah ya halitta MUTUM sai ya karrama shi, ya kuma bashi fifikon da ya banbanta shi da sauran halittu, a cikin qirarsa da halittarsa, da kuma cikin umurnin da ya ba shi, da hani; (Kuma Mutum shine) RAI (wato: RUHI) da HANKALI da JIKI.  (Shi kuma Uban Mutane; wato annabi Adamu shine) Damqa xaya daga LAKAR QASA (ta,tavo), da kuma busar rai daga RUHIN ALLAH,
"A yayin da Ubangijinka yace wa Mala'iku: Lallai ne, zan halitta wani mutum daga laka   *   Idan na daidaita shi, kuma na yi busa a gare shi daga ruhina, Sai ku faxi a gare shi, kuna masu sujjada" [Sad:  71-72].
Allah ya halicci Mutum a mafi kyan tsayuwa,      ya kuma sanya masa a cikin jikinsa HALAYYA da JI IRIN NA JIKI, tare da JIN ZAQI ko XACIN ABUBUWA.
Kuma lallai mutanen da a jikinsu suke jin Imani (abincin rai ko ruhi),
da soyayya (kayan zuci),
da tausayi (daga AXIFA);
Sune waxanda suka fi tabbatar da ma'anonin MUTUNTAKA dayawa; fiye da wassunsu, irin mutuntakar da take xaukar SALON RAYUWARTA da QIMARTA daga Musulunci.

            Musulunci ya kiyaye mutum da mutuntaka ta hanyar tsayar da haddodi na shari'a; waxanda daga cikin muhimman manufofinsu akwai: kiyaye haqqoqin xaixaikun mutane.
            Kuma musulunci ya tsarkake mutum, ya kuma xaukaka shi, a cikin da'ira ko karantarwar  alqur'ani,    Kuma duk lokacin da mutum ya kusanci Ubangijinsa da yin sallah da bauta da addu'a to sai mutuntakarsa ta xaukaka,   Allah (تعالى) yana cewa:
"Kuma ku nemi taimako da yin haquri da sallah" [Baqarah: 45]. Ya kuma ce:
"Lallai sallah tana yin hani daga alfasha da abin qi" [Ankabut: 45]. Kuma yace:
"Ka karvi sadaka daga dukiyoyinsu, kana mai tsarkake su, da kore musu dauxa da ita" [Taubah: 103].
Waxannan ibadodi ne, da suke da tasiri; Suke da tasiri ga ran mutum;  saboda suna bada tarbiyya ga mutum akan haquri da ikhlasi, suna kuma ba shiko samar masa da halayya ababen godiya, sa'annan (a ko-da yaushe) suna tsamar da shi daga sifofi ababen zargi.

            Kuma shi Musulunci a ko- da yaushe yana cikiyar abinda zai xaukaka mutum, ya kuma kawo masa kamala; ta hanyar rayar da KIYAYE ALLAH (تعالى) (a cikin mutane); Allah yana cewa:
"Kuma lallai mutum, hujja ne ga abinda ya shafi kansa, Masani    *   Kuma ko da ya jefa uzurorinsa (to ba za a karva masa ba)" [Qiyamah: 14-15].
Kuma idan Mutum ya jagoranci ransa, ya kuma yi qoqarin gyara ta to sai ta miqa wuya a gare shi, kuma sai mutumtakarsa ta yi haske, Allah (تعالى) yana cewa:
"Kuma waxannan, da suka yi qoqari ga neman yardarmu, lallai za mu shiryar da su hanyoyinmu" [Ankabut: 69].
            Kuma lallai MUTUNTAKAR da musulunci ya tsarkake; ta haxa dukkan JINSI da LAUNI, domin mutane su samu sanayyar junansu, kuma su samu sabo, su kuma rayu suna 'yan'uwa, tare da tsayar da wajibin shugabanci da mayewar wassu a bayan wassu a doron qasa, Allah (تعالى) yana cewa:
"Ya ku Mutane! Lallai ne Mu,mun halicce ku daga namiji da mace, kuma muka sanya ku dangogi da qabiloli, domin ku san juna. Lallai mafificin daraja a wurin Allah daga cikinku shine mafificinku a taqawa" [Hujuraat: 13]. Kuma Allah (تعالى) yana cewa:
"Ya kuMutane! Ku bi dokokin Ubangijinku, wanda ya halitta ku daga rai guda xaya, kuma ya halitta masa matarsa daga kansa, Kuma ya watsa daga gare su maza masu yawa da mata, Kuma ku bi Allah da taqawa, wanda ku ke roqon juna da shi, da kuma zumunci, Lallai Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne" [Nisa'i: 1].

            Kuma yana daga cikin ABINDA MUTUNTAKA take hukuntawa a cikin Musulunci: Taimakawa juna, da tallafawa, da gina ma'anonin so da rahama da tausayi da sassautawa, da kuma qauracewa qulle mutum ko riqe shi a zuci, da nisantar girman kai, da xaukar fansa, da yaudara da cin amana, da hana zalunci da taimakon mabuqaci, Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa:
"Kuma ku kasance bayin Allah 'yan'uwan juna".

            Alqur'ani mai karamci yana rayar da ma'anonin Mutuntaka masu girma, kuma yana tabbatar da girman da ya baiwa mutum, kamar yadda alqur'anin yake kare axifar so a wurin mutum daga bauxewa daga manufofinta, kuma yake kare shi daga yin jayayya abun qi, wacce ke cin karo da tausasawa tatacce dake tsakanin  mutune, sa'annan ya sanya mutum yana ganin gaskiya, kuma yana sanin shiriya, yana yin hukunci da hankali, kuma yana cikiyar a ina adalci yake,    Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa:
"Kuma ina roqonka yin adalci a cikin halin yarda da na fushi".

            A ko yaushe, Alqur'ani yana tsarkake mutum;domin kada buqatu irin na jiki da sabuban sha'awa su saukar da shi daga matakin girma, zuwa ga matakin da mutane za su wayi-gari suna masu bautawa sha'awowinsu ko neman jin daxinsu. Kuma alqur'ani yana xaukaka matsayin rayuwa; don kar ta canza zuwa ga wata jayayya abar qi, da yaquka masu halakarwa, wanda ran mutum da jikinsa zasu walaqanta a cikinSu.

            Mutuntaka a cikin musulunci ta kai wata daraja mai girma, da martaba maxaukakiya wajen manufofinta da hanyoyin tabbatar da ita,
YANA DAGA CIKIN HAKA:
Kyautata wa IYAYE guda biyu, ta hanyar karrama su, da ciyar da su, da qanqan da kai a gare su,
Da wajen kulawa da MACE, da bata haqqoqinta; UWA ce ko MATA ko 'YA ko 'YAR'UWA,   Allah (تعالى) yana cewa:
"Idan xayansu (iyaye guda biyu) a wurinka ya kai ga tsufa ko kuma dukkansu biyu, to, kada ka ce musu 'Uf', kuma kada ka tsawace su, kuma ka faxa musu Magana mai karimci" [Isra'i: 23].
Kuma Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Duk wanda aka jarrabe shi da wani abu na 'ya'ya mata, sai ya kyautata musu, to za su zame masa kariya daga faxawa wuta". Kuma yace:
"Wanda ya xauki nauyin 'yan mata biyu har suka balaga, zai zo a ranar qiyama Ni da Shi, Sai Annabi yahaxe tsakanin yatsunsa".
Kuma Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Mafificinku alkhairi shine wanda ya fi ku alkhairi ga iyalansa, kuma Ni, ne mafificinku alkhairi ga iyalaina".

            Kuma an rasa mutuntaka, an kuma shafe alamominta idan aka yi ta'addanci ga (Allah) mahalicci (جل وعلا) a cikin halittarsa, da cikin halattawa da haramtawa,    Allah (تعالى) yana cewa:
"Ya halitta mutum daga xigon maniyya sai gashi yana mai husuma bayyananniya" [Nahl: 4]. Kuma yace:
"Ya ku waxanda suka yi imani kada ku haramta abubuwa masu daxi da Allah ya halatta muku, kuma kada ku qetare iyaka, Lallai ne, Allah ba ya son masu qetare haddi" [Ma'idah: 87].

            Kuma mutum ya kan yi alfahari, da xagawa, da girman kai, da aikata abinda ya ga dama, a lokacin da ya kai zuwa ga mulki, ko aka yalwata masa ni'imomi da alkhairori,   Allah (تعالى) yana cewa:
"Lallai ne Mutum haqiqa, yana girman kai   *   Domin ya ga kansa, ya wadata" [Alaq:  6-7].
            Kuma wannan nau'i na vata –wato: girman kai, da aikata abinda mutum ya ga dama- yana kaiwa zuwa ga uquba, da bala'o'i, dasamun koma-baya, da xebe albarkar alkhairi da arziqi, wanda Allah ke shumfuxa shi ga bayinsa,  Allah (تعالى) yana cewa:
"Kuma da mutanen alqaryu sun yi imani sun bi dokoki, da, Mun buxe albarkoki akansu, daga sama, da qasa, Saidai kuma sun qaryata, sai muka kama su da abinda suka kasance suna aikatawa" [A'araf: 96].

            Kuma mutuntakar mutum bata inganta, ta kuma kasance tana da wata qima, har sai HANKALI ya 'yantu daga vata, AQIDA kuma ta 'yantu daga gaskata tatsuniyoyi da qarereyin da ake lulluvewa (wato: dajal);
YANA KUMA DAGA CIKIN HAKA;
Abinda ya ke aukuwa na sihiri, da ilimin taurari, da riya yin zance da rayukan boye, da karanta tafin hannu, da sihirin sanya barci, Duk waxannan aiyukan suna lalata mutuntakan mutum, kuma suna vata wa musulmi aqidarsa, da halayensa, kuma yarda da su yana jefar wa mutum hankalinsa da tunaninsa.

            Waxanda suke qona mutane da ransu, suke kuma yin qone-qone, da kashe masu yin sallah a masallatai, lallai haqiqa an shafe mutuntakansu, kuma basirarsu ta yi dufu.

            Kuma waxannan, da suke kutsawa,sannan su yi dauxa wa masallacin da aka yi isra'i da Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم); su yi masa dauxa da jikinsu da kuma takalmansu, sannan su karkashe mata da yara, da manyan mazajen da basa xauke da makamai a cikin filin harabar masallacin, suma zukatunsu sun mutu, kuma sun tove rigar mutuntaka da dukkan ma'anoninta da surorinta,   Allah (تعالى) yana cewa:
"Tsarki ya tabbata ga wanda ya yi tafiyar dare da bawansa, daga Masallaci mai alfarma zuwa ga Masallaci mafi nisa, wanda muka sanya albarka a gefensa domin mu nuna masa wassu daga cikin ayoyinmu, lallai ne Shi, Shine Mai ji, Mai gani" [Isra'i: 1].   Kuma Allah yace:
"Ya ku waxanda suka yi imani! Idan kun taimaki Allah, zai taimake ku, kuma ya tabbatar da dugaduganku " [muhammadu: 7].     
            Wannan shine IMANI; wanda idan mutane suka rasa shi,sa'annan suka rasa neman haskaka rayuwarsu da hasken alqur'ani to sai su gangara zuwa can quryar qasa, kuma sai hakan ya tuntsurar da qimar mutum, tare da mayar da mutum zuwa ga matsayin da yake qasa da matsayin da Allah ya ajiye mutum akansa.
            Akan haka; Kuma, lallai Musulmai suna xauke da saqo mai girma zuwa ga DUNIYA, Domin su xaukaka qimar Mutum, kuma domin su fiskanci matsalolin da suka fiskanci duniya, a lokacin da yunwa ke yaxuwa, da yawaitan sharrin cututtuka, da kuma korar miliyoyin mutane daga qasashensu da gidaddajinsu, da kuma kunnuwar wutan fitintinu;    Wannan kuma saboda kasancewar Shi musulmi, yana xauke da zuciyar da take xauke da rayayyen tausayi ga Mutum; wanda ta ke tunkuxa shi zuwa ga yaxa shiriya, da taimakon waxanda aka zalunce su, da qoqarin yaxa dawo da fata cikin jijiyar rayuwar mabuqata, da isar da taimako ga waxanda suka cutu, a sanadin wani bala'i, Hakazalika musulmi yana xauke a tare da shi, da SAQO irin na AMINCI, da TAUSAYI (rahama).
            Kuma, a lokacin da muke tunani cikin tarihin Sahabban Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) zamu ga cewa lallai su, sun bada mafi burgewan misali, a vangaren ciyarwa, da kyautatawa mutane, tare da yaxuwansu a sasanin qasar Allah mai faxi (duniya), suna shiga ko-ina, cikin tafiya mai nisa, domin su SANAR DA MUTANE MUSULUNCI, Wannan kuma ya kasance ne saboda tausayinsu ga halittu, da kuma shiryar da su zuwa ga hanyar gaskiya, tare da xaukaka lamarin mutum;   suna yin haka sunamasu neman yardar Allah.
            Suma masu yin da'awa zuwa ga Allah, a kowani zamani, da kowani wuri, da waxannan da suke bada rayukansu fiysabillahi, da dukiyarsu don yin biyayya wa Allah, da waxannan da suke tsaye akan aiyukan alkhairi, da haddatar da Mutane alqur'ani da karantar da shi, da waxannan da suka kakkafa kayukansu don amfanar da wassunsu,   Dukkan waxancan lallai Allah ya azurta su da mutumtaka da tausayi na gaskiya, da cikakken ji da irin abinda Mutane suke ji da shi (na damuwa ko daxi); Kuma Alqur'ani shi ya tarbiyyantar da su akan haka,   saboda haka; Muna yi muku murnar jin daxin rayuwar duniya, da kuma rabauta da ni'ima mai tabbata (a lahira).

            Kuma lallai ma'anonin mutuntaka da tausayi suna bayyana a wajen jagororin wannan qasa, da mutanenta, saboda gudumawa mai girma da suke bayarwa ga Mutum, wanda kuma yake qarfafa aikin agazawa, a wurare dayawa a faxin duniya.      Kuma suma sauran Musulmai a wurare dayawa a faxin duniya basu taqaita qoqarinsu ba, a wajen fara gabatar da kayan agaji, ga waxanda aka zalunta, da waxanda musiba ta shafa, tare da miqa hannun taimako ga kowani mabuqaci, suna masu nuna mutuntaka ta gaskiya, da ji da irin abinda mutane suke ji da shi (na daxi, ko wahala).   Allah (تعالى) yana cewa:
"Kuma don me bai kutsa cikin al'aqabah?   *   Kuma menene ya sanar da kai abinda ake ce wa al'aqabah?'   *    Itace fansar wuyan bawa    *   Ko kuma ciyarwa a cikin wani yini ma'abocin yunwa  *    Ga maraya, ma'abocin zumunta    *   Ko kuwa ga miskini ma'abocin turvaya (wanda babu komai a wurinsa)" [Balad: 11-16].

            Allah yayi mini albarka NI da KU, cikin alqur'ani mai girma, ya kuma amfanar da NI da KU da abinda ke cikinsa na ayoyi, da tunatarwa mai hikima,      Ina faxar maganata wannan, kuma ina neman gafarar Allah mai girma ga Ni da KU da kuma sauran Musulmai, ku nemi gafararSa,    lallai shi Mai gafara ne Mai rahama.
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,
>>> 
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,

HUXUBA TA BIYU
     Godiya ta tabbata ga Allah; yabo Mai yawa, Mai daxi, Wanda yake cike da albarka, Ina yin godiya a gare shi –tsarki ya tabbata a gare shi- kuma ina yaba masa, Kuma ina shaidawababu abin bautawa da gaskiya sai Allah; shi kaxai yake bashi da abokin tarayya, Kuma ina shaidawa lallai shugabanmu kuma annabinmu Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa ne, Allah yayi daxin salati da sallama a gare shi, da iyalansa da sahabbansa,
Bayan haka:
Ina yi muku wasici da ni kaina da bin dokokin Allah; saboda ita taqawa garkuwa ce mai bada kariya, kuma a cikin aikatata, akwai samun rabo mai girma.

            Kuma YANA DAGA CIKIN abubuwan da suke munana mutuntaka, su kuma gurvata haqiqaninta: Amfani da tsananin da mutane suka samu kayukansu a ciki, da halin qunci, da buqatar mabuqata wajen mu'amala da riba,     Kuma lallai Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya bayyana sakamakon Mutane masu yin mu'amala da riba; a inda yace:
"A wannan daren na yi mafarkin wassu mutane guda biyu waxanda suka zo mini, sai suka fitar da ni zuwa ga qasa mai tsarki, Sai muka tafi har sai da muka iso wani kogi na jini, wanda a cikinsa akwai wani mutum yana tsaye, A gavar kogin kuma ga wani mutum yana tsaye, a gaba gare shi akwai duwatsu , Sai mutumin da yake cikin kogin ya fiskanto, har idan ya so ya fita, Sai wannan mutumin da ke gavar kogin ya jefe shi da dutse a bakinsa, sai ya mayar da shi can inda ya ke, Sai ya zama duk lokacin da ya nufi ya fita sai ya jefe shi a bakinsa da dutse, sai ya koma wurinsa na farko da ya kasance, Sai nace: Wanene wannan wanda yake cikin kogin? Sai yace: Maciyin riba ne"    [Bukhariy ya ruwaito shi].

HUXUBAR TA QARE
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,

Sai ku yi salati, -Ya ku bayin Allah- ga Manzon shiriya, saboda Allah ya umurce ku da aikata haka, a cikin littafinsa; a inda yake cewa:
"Lallai Allah da Mala'ikunsa suna yin salati ga wannan annabin, Ya ku waxanda suka yi Imani, ku yi salati a gare shi, da sallama na aminci" [Ahzab: 56].

Ya Allah! kayi salati wa Annabi Muhammadu da iyalanSa da zurriyarSa, kamar yadda kayi salati wa iyalan annabi Ibrahima, kuma ka yi albarka wa Annabi Muhammadu da iyalanSa da zurriyarSa, kamar yadda kayi albarka wa iyalan annabi Ibrahima, lallai kai Abun godiya ne, Mai girma.
            Ya Allah! Ka yarda da khalifofi guda huxu shiryayyu;    Abubakar da Umar da Usmanu da Aliyu,    da Iyalan annabi da sahabbansa masu karamci, ka haxa da mu da baiwarka, da rahamarka, Ya mafificin masu rahama.
            Ya Allah! ka xaukaka musulunci da musulmai, Ya Allah! ka xaukaka musulunci da musulmai, kuma ka qasqantar da kafirci da kafirai, kuma Ya Allah! Ka ruguza kafirci da kafirai, kuma Ya Allah! Ka sanya wannan qasar ta zama da aminci, cikin nitsuwa, da sauran qasashen musulmai.
            Ya Allah! Lallai mu muna roqonka aljanna, da abinda yake kusantarwa zuwa gare ta, na zance ko na aiki, kuma muna neman tsarinka daga wuta, da kuma abinda yake kusantarwa zuwa gare ta na zance ko na aiki.
            Ya Allah! Lallai mu muna roqonka mabuxan alkhairi da qarshensu, da abinda ya tattara su, da farkonsu da qarshensu, kuma muna roqonka darajoji maxaukaka a cikin aljanna, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Ka gyara mana addininmu wanda shine kariya ga al'amarinmu, kuma ka gyara mana duniyarmu wacce a cikinta rayuwarmu take, kuma ka gyara mana lahirarmu wacce zuwa gare ta za mu koma, ka sanya rayuwa ta zama qarin alkhairi ne a gare mu, mutuwa kuwa ka sanya ta hutu ne a gare mu daga kowani sharri. Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Lallai mu muna roqonka shiriya da taqawa da kamewa da wadaci da arziqi.
            Ya Allah! Ka taimake mu kada ka taimaki wassu akanmu, ka bamu nasara kada ka bada nasara ga wassu akanmu, ka qulla mana, kada ka qulla ma wassu akanmu, ka shirye mu, kuma ka sauqaqe shiriyarka a gare mu, kuma ka taimake mu akan wanda ya yi zalunci akanmu.
            Ya Allah! Ka sanya mu zama masu ambatonka, masu yin godiya a gare ka, masu qanqan da kai a gare ka, masu yin kuka da mayar da al'amari zuwa gare ka.
            Ya Allah! Ka karvi tubanmu, ka wanke zunubanmu, ka tabbatar da hujjojinmu, kuma ka daidaita harshenmu, ka zare dauxar zukatanmu.
            Ya Allah! Lallai mu muna neman tsarinka daga gushewar ni'imarka, da canzuwar lafiyarka, da zuwan azabarka kwatsam, da kuma dukkan abinda zai sanya ka fushi.
            Ya Allah! Ka shumfuxa mana albarkokinka da rahamarka da falalarka da arziqinka.
            Ya Allah! Ka yi mana albarka cikin shekarunmu, kuma ka sanya mana albarka cikin matanmu, da 'ya'yanmu, da zurriyarmu, da aiyukanmu da shekarunmu, ka sanya mu; mu zama masu albarka a duk inda muke, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Lallai mu muna roqonka tabbatuwa cikin lamarin addini, da kuma azama akan aikin shiriya, da ribatar kowace biyayya, da kuvuta daga kowani savo, da rabauta da aljanna, da kuvuta daga wuta.
            Ya Allah! Ka taimaki wanda ya taimaki addini, kuma ya Allah ka tavar da duk wanda ya tavar da musulunci da musulmai, Ya Allah! Ka taimaki addininka da littafinka da sunnar annabinka da kuma bayinka muminai.
            Ya Allah! Ka kasance wa musulmai… a kowani wuri, Ya Ubangjin talikai, Ya Allah! ka kasance wa musulmai… a qasar Sham Ya mafificin masu jin qai, Ya Allah! Ka kasance musu Mai qarfafawa, Mai taimako, Mai tallafawa, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Ubangijin gaskiya, Ya Allah wanda ya saukar da littatafai, mai gudanar da gajimare, wanda ya rusa rundunoni, ka kwace nasara daga maqiyanka; maqiyan addini, kuma ka taimaki musulmai akansu, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Ya Mai qarfi, Ya Mabuwayi! Ka taimaki musulunci da ma'abotansa, a kowani wuri.
            Ya Allah! Ka yi rahama ga mamatanmu, ka bada lafiya ga majinyatanmu, ka yaye baqin cikinmu, ka sunce fursunoninmu, ka jivinci lamarinmu, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Ka yi dace wa shugabanmu da abinda kake so, kuma ka yarda, Ya Allah ka datar da shugabanmu mai hidimar harami guda biyu zuwa ga abinda kake so, kuma ka yarda, ka datar da shi zuwa ga shiriyarka, kuma ka sanya aikinsa ya zama cikin yardarka, Ya Ubangijin halittu, Kuma ina roqonka ka datar da na'ibansa guda biyu zuwa ga abinda kake so, kuma ka yarda, lallai kai mai iko ne akan  komai.
            Ya Allah! Ka datar da jagororin musulmai gabaxaya wajen yin aiki da littafinka, da yin aiki da shari'arka, Ya mafificin rahamar masu rahama.
            Ya Allah! Kai ne abin bauta; babu abin bautawa da gaskiya sai kai, kai ne Mawadaci mu kuma faqirai, ka saukar mana da ruwan sama, kada ka sanya mu daga cikin masu xebe tsammani, Ya Allah! ka bamu ruwa, Ya Allah! ka bamu ruwa, Ya Allah! ka bamu ruwa, Ya Allah! Shayarwar rahama, ba shayarwar azaba ko bala'i ko rusau, ko dulmuya ba, Ya Allah! Ka rayar da garurruka da shi, ka bada ruwan sama ga bayi, ka sanya shi ya kai birni da qauye, Ya mafificin rahama masu rahama.
            "Ya Ubangijinmu! Mun zalunci kayukanmu idan baka gafarta mana, ka yi mana rahama ba to zamu kasance daga cikin masu hasara" [A'araf: 23].
            "Ya Ubangijinmu! Ka gafarta mana da 'yan'uwanmu da suka rigaye mu da imani, kada ka sanya a cikin zuciyarmu wani qulli ga waxanda suka yi imani; Ya Ubangijinmu lallai kai ne Mai tausasawa ne Mai rahama" [Hash,ri: 10].
            "Ya Ubangijinmu! Ka bamu mai kyau a duniya, kuma ka bamu mai kyau a lahira, ka kare mu daga azabar wuta" [Baqarah: 201].

"Lallai Allah yana yin umurni da adalci, da kyautatawa, da baiwa makusanci, kuma yana yin hani akan alfasha da abin qi, da zalunci, Yana muku wa'azi da fatan zaku zama masu tunawa" [Nahli: 90].
Ku riqa ambaton Allah zai riqa ambatonku, ku gode masa akan ni'imominSa zai muku qari, kuma ambaton Allah shine mafi girma, kuma lallai Allah ya san abinda kuke aikatawa.
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,


2015/11/02

MATASA MANYAN GOBE الشباب عدة الأمل Hudubar Masallacin Annabi saw ta Assubaitiy juma'a 15 Jumadal ula 1436hijira








HUXUBAR MASALLACIN ANNABI (صلى الله عليه وسلم)
JUMA'A,15/JUMADAL ULA/1436H

MAI TAKEN
MATASA MANYAN GOBE
(الشباب عُدّة الأمل)



LIMAMI MAI HUXUBA
SHEHIN MALAMI DR. ABDULBARIY XAN AWWADH AS-SUBAITIY







TARJAMAR
ABUBAKAR HAMZA
بسم الله الرحمن الرحيم
Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijina, Babu abin bautawa idan ba shi ba,  akansa na dogara, kuma zuwa gare shi ake tuba, Ina yin yabo a gare shi, tsarki ya tabbata a gare shi, kuma ina gode masa akan ni'imar lafiya datasamartaka.
Kuma ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; shi kaxai ya ke bashi da abokin tarayya, kuma babu mai warware hukuncinSa, Shine mai saurin hisabi.     
Kuma ina shaidawa lallai shugabanmu kuma annabinmu Muhammadu bawanSa ne kuma manzonsa;  yayi hanikan fasiqanci da zage-zage.
Allah ya yi qarin salati a gare shi, da iyalansa da sahabbansa, ma'abota hankali da tunani.

Bayan haka:
Ina yin wasiyya a gare KU, da NI kaina da bin dokokin Allah,     Allah yana cewa:
"Ya ku waxanda suka yi imani ku kiyaye dokokin Allah, iyakar kiyayewa, kuma kada ku mutu face kuna musulmai" [Ali-imrana: 102].

            YANAYIN SAMARTAKA YANAYI NE NA KAZAR-KAZAR, KUMA ZAMANI NE NA AIKI, SANNANLOKACINJIN DAXIN IBADA,
            Tarihi ya rubuta matsaya masu yawa kuma madawwama, ga wassu daga cikin MATASA; waxanda suka san Ubangijinsu, sannan suka yi riqo da addininsu;     Sai Qur'ani ya tabbatar da ambatonsu;    Allah mabuwayi da xaukaka yana faxa dangane da annabi Ibrahima (عليه السلام):
"Mun ji wani MATASHI yana aibanta su, anace da shi: Ibrahima" [Anbiya'i: 60].
Ya kuma faxa, dangane da ma'abota kogo:
"Lallai su MATASA ne waxanda suka yi imani da Ubangijinsu, sai muka qara musu shiriya   *  Kuma muka yi xauri akan zukatansu; a lokacin da suka tashi sai suka ce: Ubangijinmu shine Ubangijin sammai da qassai,  baza mu yi bauta wa wani abin bauta idan bashi ba,   Lallai idan muka yi haka, mun faxi zalunci" [Kahfi: 13-14].

            MATASA sune tanadin da ake qulla buri akansu, sannan sune burin al'ummomi domin rayuwar gobe da ake fiskanta, suna da matsayi mai girma a cikin addinin Musulunci, kuma suna daga cikin mutane guda bakwai; waxanda Allah zai sanya su a cikin inuwarSa ranar da babu wata inuwa sai tasa "Da SAURAYIN da ya taso cikin bautar Allah".

            Shekarun samartaka qarfi ne da yake da tasiri ga al'ummomi, kuma samartaka azamace da iko da qarfi, da nashaxi,  Lallai kuma waxannan sifofin suna hukuntawa SAURAYI ya yi qoqarin jagorantar rayuwarsa; da kansa, cikin hikima, yana mai kiyaye kansa, tare da sanya linzami wa ransa, ko dabaibayi ko birki; don ya hana ta sauri, sannan ya fiskantar da kansa zuwa ga aiyukan alkhairi da samun rabo, kuma ana son saurayi ya zana wa kansa ko ya tsara wassu manufofin da yake fatan cimma su a rayuwarsa, waxanda zai yi ta hawa matakan xaukaka da su, har kuma ya iya bada gudumawarsa a rayuwar mutane, tare da tabbatar da wata manufa ko isar da wani saqo, a bayan qasa.
            Kuma tabbas idan a rayuwar matasalamarin MANUFA ya zagwanye,to sai rayuwarsu ta wayi gari bata da wata qima, sa'annan abubuwan da matasan suke basu muhimmanci su zama tauyayyu da naqasa, "Rayuwar duniya ba komai ba ce, face abar shagala da wasa, kuma lallai lahira tabbas itace rayuwa, da sun kasance suna sani" [Ankabut: 64].

            LOKACIshine mafi tsadan abinda saurayi a rayuwarsa yake mallaka, kuma a cikin lokacin saurayi yake shuka burace-buracensa, yake kuma qoqarin tabbatar da manufofinsa; ta hanyar neman ilimi mai amfani, da aiki managarci, da yin ibada da xa'a, da samun nau'ukan wayewa mabanbanta masu fa'ida, da yin aiyuka masu muhimmanci masu haske, waxanda za su zama ma'auni ga manufofinsa da aiyukansa, kuma su bunqasa masa rayuwarsa a gare shi. Kuma a cikin lokacin,Saurayi yake kwarewa cikin wata sana'a wacce zata bunqasa gwanancewarsa, da kuma wassu aiyukan da zai iya gina ko xora rayuwarsa akansu.

            Kuma idan lokacin samari ya wofanta daga manufofi maxaukaka, to sai munanan aqidunda suke zamar da MATASAko karkatar da su, su silale; zuwa gare su, Sai MATASAsu shagalta da abubuwan da basu da qima, da kuma tunani cikin yasassun al'amura, Daga nan, sai sabuban vatansu daga miqaqqiyar turba su yi qarfi.

Kuma lallai rashin aikin yi (ga matasa), da zaman banza:Sune gona mai yabanya; wacce ake shuka dukkan sharri, da dangin nau'ukan vata.
Imam Asshafi'i (رحمه الله) yace: "Rai, idan baka shagaltar da ita da gaskiya ba, to sai ta shagaltar da kai da varna".

            Kuma yana da hatsari: Vata lokacin da ake yi wajen yawo tsakanin shafukan sada zumuncinda suke cutar da aqida, suke kuma yin tasiri ga halayya,ko rikita su, suke kuma raunata alaqoqin da suka qulle tsakanin iyalai, ta hanyar sanya mutum cikin rayuwar kaxaici alhalin yana cikin jama'a. Kuma mummunan tasirin waxannan lamuran abu ne, da yake a fili; baya vuya.

            MATASA suna fiskantar makirce-makirce daga maqiya addini; ta hanyar bijiro musu abubuwan sha'awa na haram da kuma ruxinsu, da nufin shafe musu abin alfaharinsu (addini), tare da vata musu ko tuntsurar da abinda suka fiskanta na kyakkyawiyar rayuwa, da qoqarin ruguza musu samartakarsu,  da kuma jefa su cikin ximuwa da vata, da kawar da hankulansu daga himmatuwa da cinma burace-buracensu maxaukaka, da muhimman lamuran garurrukansu da al'ummarsu (musulma).
            Tsira kuma zata kasance ne kawai cikin yin tarbiya wa rai da (littafin Allah) alqur'ani, da baiwa zuciya abincin imani, da yin tafiya cikin tawagar salihan bayi.

Shi kuma qosar da sha'awowi ko buqatu ta hanyoyin da aka shar'anta:Na tabbatar wa mutum moriya, da cin nasara da karama.
            Saboda shi AURE ga MATASA buqata ce ta halitta, kuma ya kan zama nitsuwa ga rai, sannan aure garkuwa ne ga xabi'ar saurayi da halayyarsa.Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa:
"Ya ku taron MATASA! Duk wanda ya samu iko a cikinku sai ya yi aure, saboda aure shi ya fi rintsar da ido, kuma ya fi bada garkuwa ga farji. Wanda kuma bai samu iko ba to sai ya lazimci azumi; saboda azumi kamar fixiya ne a gare shi".
            Shi kuma jinkirta aure ga wanda yake da ikon yinsa yana da irin nasa cutarwar; ga halayyan mutum da kuma rai, da kuma wassu cutarwar ga xaukacin al'umma.  Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa:
"Idan wanda kuka yarda da addininsa da halayyarsa ya zo muku, to ku aurar masa, Idan ba ku aikata haka ba, to fitina zata kasance a bayan qasa, da kuma varna mai faxi".

            Saurayi yana da buqatar a rayuwarsaya riqa daidaita tsakanin aiki da hankali da kuma axifar soyayya, Wannan kuma saboda kasancewar zamanin samartaka = yanayi ne da axifar soyayya mai yawa take ruruwa a cikinsa, wanda kuma za su iya yin mummunan tasiri a rayuwar saurayi ta gobe da yake fiskanta, idan har ba a tankwara ta ga hasken Qur'ani, ko abinda hankali ke hukuntawa ba.
Kuma lallai axifar so ko ta qi matsananci, wanda babu hasken wahayi a cikinta, tana iya jagorantar saurayi zuwa ga qetare iyaka, ko zuwa ga taqaitawa, ko izuwa ga bauxe wa hanya, ko ga yin qari ga addini.
            Kuma ana magance matsalar axifar so da take da qarfi a wajen saurayi, ta hanyar qosar masa da ita a cikin iyalansa, da jiyar da shi, ko kuma kewaye saurayi da yanayi na bada kulawa, da kuma bada aminci, tare da tarbiyantar da ransa akan kamewa, da kuma rintse idanu, tare da jin kunyar Allah (تعالى).
An ruwaito daga Jarir xan Abdullahi yace: Na tambayi Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) dangane da gani na bazata, Sai ya umurce ni da na kawar da ganina.
Kuma Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Ya kai Aliyu! Kada ka biyar da gani akan gani, saboda ganin farko naka ne, amma na qarshen banaka ba ne".

            Kuma yana daga abinda yake taimaka wa MATASA wajen gina mutum qaqqarfa mai amfani: Gina ko qarfafa alaqarmatasan da iyalansu; kasancewar iyalai sune garkuwan samari, kuma sune mafaka a gare su, wanda ke samar da nitsuwar zuci a gare su, da hutu, da kwanciyar hankali.  Kuma saboda kasancewar iyalai sune matabbatar nasiha da faxakarwa ga 'ya'yansu, da yin tarbiyya irin ta imani a gare su, tare da qarfafarsu. Yayin da rashin iyalai ko yin watsi da su, ko kuma samun raunin alaqar da ke tsakanin iyaye da 'ya'yansu, ke kai MATASA xaukar tarbiyyarsu daga wuraren renon da aka jahilta, da kuma qungiyoyin da za su shafe hankulansamari, sannan su jefa su cikin ramukan vata masu nisa.

            Yin wa'azi da faxakarwa a rayuwar saurayi sune abinci ga ruhinsa (zuciya), da samun nitsuwa a ransa,  Kuma lallai alqur'ani ya qarfafa hakan; saboda kasancewarsa abu mai muhimmanci wajen gina mutum lafiyayye, tare da amintar da takunsa a cikin duniyarsa, Ya zo a cikin wasiyyoyin annabi Luqmanu ga xansa,  "Kuma yayin da Luqmanu yace wa xansa, a lokacin da yake masa wa'azi; Ya kai qaramin xana! kada ka yi shirka wa Allah, lallai haxa Allah da wani zalunci ne mai girma" [Luqman: 13].
Sannan ya ce: "Ya kai qaramin xana! Lallai aiki idan ya kasance koda gwargwadon kwayar komayya ne, sai ya kasance a cikin wani dutse, ko a cikin sammai ko a cikin qassai, to Allah zai zo da shi, Lallai Allah Mai tausasawa ne Masani    *    Ya kai qaramin xana! Ka tsayar da sallah, kuma ka yi umurni da kyakkyawa, kuma ka yi hani ga mummuna, sannan ka yi haquri game da abinda zai same ka, Lallai wannan yana daga muhimman al'amura" [Luqman: 16-17].

            Irin aikin da saurayi zai yi; ta hanyar tafiya a sasannin qasa, (don rufa wa kansa asiri) wannan xaukaka ne ga mutuncinsa, kuma karama ce ga iyalansa,   daxin daxawa kuma aikata hakan shine mafi daxin hanyoyin neman arziqi;   An tambayi Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) cewa Wani aiki ne ya fi daxi? Sai ya ce:
"Aikin mutum da hannunsa, da kuma kowani kasuwanci na halal kuvutacce".
Kuma Annabi (صلى الله عليه وسلم) ya sanya tara itatuwa da sayar da su a matsayin abinda yafi alkhairi ga mutum, akan ya roqi mutane; sun ba shi ko sun hana shi.
Kuma Umar (رضي الله عنه) yana cewa:
"Na kan ga saurayi sai ya burge ni, amma idan aka ce: Bashi da wata sana'a to sai qimarsa ta zube  daga idona". Sa'annan yana cewa:
"Kada wani daga cikinku ya zauna ya qi neman arziqi; sai yayi ta cewa: Ya Allah! Ka azurta ni; Ai kun san cewa sama bata zubo da ruwan zinari ko azurfa".
            Kuma lallai saurayi mai manufa ya kan qaurace wa zaman banza, sai ya fiskanci yin aiki; koda kuwa yaya nau'in aikin yake, ba tare da ya raina wata sana'a aiyananniya, ko wani aiki sananne ba.
            Su kuma al'umma da dukkan vangarorinsu ana nemansu da su sauqaqe hanyoyin samun aiyukan da suka dace, tare da bubbuxe qofofin kasuwanci, domin samari su zama masu amfanar da kansu, da garurrukansu da al'ummarsu.
           
            Kuma ya dace ga saurayi cikin saukansa da tashinsa, da tafiyarsa (wassu qasashen) da zamansa (a garinsu, ko qasarsu):Ya zamto mai alfahari da addininsa da al'adarsa, da riqa jin xaukakar aqidarsa; kada ya riqa jinkunyar bayyanar da musuluncinsa.Kuma da aikata haka ne kawai; zai qetare qullin jin naqasa, da makauniyar bin maqiyan Allah, Allah ta'alah yana cewa:
"Kuma jin izza na Allah ne da ManzonSa da kuma muminai" [Munafiquna: 8].

            Nitsuwa a rayuwar saurayi hali ne abun yabo, kuma xabi'a ce da za a iya kwaikwayarta, kuma wani qarfi ne da ke nuna hankalin wanda ya siffanta da ita.
Shi kuma tsanani cikin mu'amala, da halin tunzura, ko neman xaukar fansa, dukkansu alamomi ne masu hatsari, sannan kuma fizga ne irin naShexan, waxanda muninsu zai iya cutar da samari, ya kuma tunkuxar da qarfinsu, kamar yadda hakan zai zama matsala ga al'umma gabaxayanta.

Kuma wajibi ne akan saurayi, a lokacin jin qarfi da samartaka da nashaxi;Ya kula da sunnar rayuwa, da canzuwar yanayi da hali, da tafiyan dare da yini; sai ya yi aiki a samartakanta saboda tsufansa, da kuma lokacin lafiyarsa saboda cutarsa, kuma kada ya ruxu da halin qarfi da yake ciki; saboda samartaka tsufa ne ke biye da ita, qarfi kuma yakan tafi zuwa ga rauni, kamar yadda ita kuma lafiya cuta ke yi mata barazana, Allah ta'alah yana cewa:
"Allah shine wanda ya halitta ku daga rauni, sa'annan ya sanya wani qarfia bayan raunin, sa'annan ya sanya a bayan qarfin wani rauni da furfura, yana halittar abinda ya yi nufi, Shine Masani Mai qudura" [Rum: 54].

            Allah yayi mini albarka NI da KU, cikin alqur'ani mai girma, ya kuma amfanar da NI da KU da abinda ke cikinsa na ayoyi, da tunatarwa mai hikima,      Ina faxar maganata wannan, kuma ina neman gafarar Allah, ku nemi gafararSa,    lallai shi Mai gafara ne Mai rahama.
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,
>>> 
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,

HUXUBA TA BIYU
            Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai  * Mai rahama mai jin qai  * Mamallakin ranar sakamako.
Kuma ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah; shi kaxai yake bashi da abokin tarayya,  abun bautan na farko da na qarshe.
Kuma ina shaidawa lallai shugabanmu kuma annabinmu Muhammadu bawansa ne kuma manzonsa, majivincin masu taqawa.

            Bayan haka;
            Ina yin wasici a gare KU, da NI kaina da bin dokokin Allah, Allah (تعالى) yana cewa:
"Kuma ku bi dokokin Allah, sai Allah ya ilmantar da ku" [Baqara: 282].

            Shi saurayi musulmi zuciyarsa ta kan cika da son Allah da son Manzonsa (صلى الله عليه وسلم), Kuma da zai dulmuya cikin wani abu na savo,to da saizuciyarsa ta yimotsi da jin tsoron Allah, da kuma nadama akan wannan zunubin, Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa:
"Lallai bawa idan ya aikata kuskure sai a xiga wani baqin xigo a cikin zuciyarsa, idan kuma ya bari sannan ya tuba sai a kankare zuciyarsa, idan kuma ya koma wa zunubin; to sai a qara wannan alamar, har sai ta rufe zuciyar, kuma shine tsatsar da Allah ya ambata; ((A'aha! kawai dai; ya sanya tsatsa ne akan zuciyarsu abinda suka kasance suke aikatawa)) [Muxaffifina: 14]".

            Wassu samarin sun riski kuma sun gane kuskurensu, kuma tabbas sun san haramcin abinda suke aukawa cikinsu, saidai kuma suna jinkirta tuba, kuma suna cewa da-sannu, da-sannu; Shi kuma faxin haka; -ma'ana: da, sannu zan dena, da sannu zan tuba- shine mafi girman abinda ke hana mutum tuba, kuma faxin (Da sannu) runduna ne daga cikin rundunonin shexan.

            Shi kuma dogewar wassu MATASA cikin zunubai yana dahatsari mai girma, kuma sharri ne mai bazuwa.
            Kuma lallai mai hankali yana jin tsoron matsalar savo, kasancewar wutan savo yana ci ne ta qarqashin toka;   saboda zai yiwu a jinkirta uqubansa, kamar yadda zai yiwu uqubar ta zo da gaggawa, Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Lallai Allah yana yin talala wa azzalumi, har idan ya tashi kama shi, ba zai suvuce masa ba. Sannan sai ya karanta: ((Kuma haka, kamun Ubangijinka ya ke; idan zai kama alqarya alhalin tana zalunci, lallai kamunsa mai raxaxi ne mai tsanani)) [Hudu: 102]".
Kuma manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Idan kaga Allah yana baiwa bawa duniya akan savonsa abinda yake so, to lallai wannan talala ne. Sannan sai Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) ya karanta: ((Yayin da suka mance abinda aka tunatar da su, sai muka bubbuxe qofofin kowani abu a gare su, har sai da suka yi farin ciki da abinda aka basu sai muka kama su, kwatsam, sai ga su sun xebe tsammanin dukkan alkhairi)) [An'am: 44]".

            Sai ku yi salati, -Ya ku bayin Allah- ga Manzon shiriya, sabodaAllah ya umurce ku da aikata haka, a cikin littafinsa; a inda yake cewa:
"Lallai Allah da Mala'ikunsa suna yin salati ga wannan annabin, Yaku waxanda suka yi Imani, ku yi salati a gare shi, da sallama na aminci" [Ahzab: 56].

Ya Allah! kayi salati wa Annabi Muhammadu da iyalanSa da zurriyarSa, kamar yadda kayi salati wa iyalan annabi Ibrahima, kuma ka yi albarka wa Annabi Muhammadu da iyalanSa da zurriyarSa, kamar yadda kayi albarka wa iyalan annabi Ibrahima, lallai kai Abun godiya ne, Mai girma.
            Ya Allah!Ka yarda da khalifofi gudahuxu shiryayyu;    Abubakar da Umar da Usmanu da Aliyu,    da Iyalan annabi da sahabbansa masu karamci, ka haxa da mu da baiwarka, da rahamarka, Ya mafificin masu rahama.
            Ya Allah! ka xaukaka musulunci da musulmai, Ya Allah! ka xaukaka musulunci da musulmai, kuma ka qasqantar da kafirci da kafirai, kuma Ya Allah! Ka ruguza kafirci da kafirai, kuma Ya Allah! Ka sanya wannan qasar ta zama da aminci, cikin nitsuwa, da sauran qasashen musulmai.
            Ya Allah! Lallai mu muna roqonka aljanna, da abinda yake kusantarwazuwa gare ta, na zance ko na aiki, kuma muna neman tsarinka daga wuta, da kuma abinda yake kusantarwa zuwa gare ta na zance ko na aiki.
            Ya Allah! Lallai mu muna roqonka mabuxan alkhairi da qarshensu, da abinda ya tattara su, da farkonsu da qarshensu, kuma muna roqonka darajoji maxaukaka a cikin aljanna, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Ka gyara mana addininmu wanda shine kariya ga al'amarinmu, kuma ka gyara mana duniyarmu wacce a cikinta rayuwarmu take, kuma ka gyara mana lahirarmu wacce zuwa gare ta za mu koma, ka sanya rayuwa ta zama qarin alkhairi ne a gare mu, mutuwa kuwa ka sanya ta hutu ne a gare mu daga kowani sharri. Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Lallai mu muna roqonka shiriya da taqawa da kamewa da wadaci da arziqi.
            Ya Allah! Ka taimake mu kada ka taimaki wassu akanmu, ka bamu nasara kada ka bada nasara ga wassu akanmu, ka qulla mana, kada ka qulla ma wassu akanmu, ka shirye mu, kuma ka sauqaqe shiriyarka a gare mu, kuma ka taimake mu akan wanda ya yi zalunci akanmu.
            Ya Allah! Ka sanya mu zama masu ambatonka, masu yin godiya a gare ka, masu qanqan da kai a gare ka, masu yin kuka da mayar da al'amari zuwa gare ka.
            Ya Allah! Ka karvi tubanmu, ka wanke zunubanmu, ka tabbatar da hujjojinmu, kuma ka daidaita harshenmu, ka zare dauxar zukatanmu.
            Ya Allah! Lallai mu muna neman tsarinka daga gushewar ni'imarka, da canzuwar lafiyarka, da zuwan azabarka kwatsam, da kuma dukkan abinda zai sanya ka fushi.
            Ya Allah! Ka shumfuxa mana albarkokinka da rahamarka da falalarka da arziqinka.
            Ya Allah! Ka yi mana albarka cikin shekarunmu, kuma ka sanya mana albarka cikin matanmu, da 'ya'yanmu, da zurriyarmu, da aiyukanmu da shekarunmu, ka sanya mu; mu zama masu albarka a duk inda muke, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Lallai mu muna roqonka tabbatuwa cikin lamarin addini, da kuma azama akan aikin shiriya, da ribatar kowace biyayya, da kuvuta daga kowani savo, da rabauta da aljanna, da kuvuta daga wuta.
            Ya Allah! Ka taimaki wanda ya taimaki addini, kuma ya Allah ka tavar da duk wanda ya tavar da musulunci da musulmai, Ya Allah! Ka taimaki addininka da littafinka da sunnar annabinka da kuma bayinka muminai.
            Ya Allah! Ka kasance wa musulmai… a kowani wuri, Ya Ubangjin talikai, Ya Allah! ka kasance wa musulmai… a qasar Sham Ya mafificin masu jin qai, Ya Allah! Ka kasance musu Mai qarfafawa, Mai taimako, Mai tallafawa, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Ubangijin gaskiya, Ya Allah wanda ya saukar da littatafai, mai gudanar da gajimare, wanda ya rusa rundunoni, ka kwace nasara daga maqiyanka; maqiyan addini, kuma ka taimaki musulmai akansu, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Ya Mai qarfi, Ya Mabuwayi! Ka taimaki musulunci da ma'abotansa, a kowani wuri.
            Ya Allah! Ka yi rahama ga mamatanmu, ka bada lafiya ga majinyatanmu, ka yaye baqin cikinmu, ka sunce fursunoninmu, ka jivinci lamarinmu, Ya Ubangijin talikai.
            Ya Allah! Ka yi dace wa shugabanmu da abinda kake so, kuma ka yarda, Ya Allah ka datar da shugabanmu mai hidimar harami guda biyu zuwa ga abinda kake so, kuma ka yarda, ka datar da shi zuwa ga shiriyarka, kuma ka sanya aikinsa ya zama cikin yardarka, Ya Ubangijin halittu, Kuma ina roqonka ka datar da na'ibansa guda biyu zuwa ga abinda kake so, kuma ka yarda, lallai kai mai iko ne akan  komai.
            Ya Allah! Ka datar da jagororin musulmai gabaxaya wajen yin aiki da littafinka, da yin aiki da shari'arka, Ya mafificin rahamar masurahama.
            Ya Allah! Kai ne abin bauta; babu abin bautawa da gaskiya sai kai, kai ne Mawadaci mu kuma faqirai, ka saukar mana da ruwan sama, kada ka sanya mu daga cikin masu xebe tsammani, Ya Allah! ka bamu ruwa, Ya Allah! ka bamu ruwa, Ya Allah! ka bamu ruwa, Ya Allah! Shayarwar rahama, ba shayarwar azaba ko bala'i ko rusau, ko dulmuya ba, Ya Allah! Ka rayar da garurruka da shi, ka bada ruwan sama ga bayi, ka sanya shi ya kai birni da qauye, Ya mafificin rahama masu rahama.
            "Ya Ubangijinmu! Mun zalunci kayukanmu idan baka gafarta mana, ka yi mana rahama ba to zamu kasance daga cikin masu hasara" [A'araf: 23].
            "Ya Ubangijinmu! Ka gafarta mana da 'yan'uwanmu da suka rigaye mu da imani, kada ka sanya a cikin zuciyarmu wani qulli ga waxanda suka yi imani; Ya Ubangijinmu lallai kai ne Mai tausasawa ne Mai rahama" [Hash,ri: 10].
            "Ya Ubangijinmu! Ka bamu mai kyau a duniya, kuma ka bamu mai kyau a lahira, ka kare mu daga azabar wuta" [Baqarah: 201].

"Lallai Allah yana yin umurni da adalci, da kyautatawa, da baiwa makusanci, kuma yana yin hani akan alfasha da abin qi, da zalunci, Yana muku wa'azi da fatan zaku zama masu tunawa" [Nahli: 90].
Ku riqa ambaton Allah zai riqa ambatonku, ku gode masa akan ni'imominSa zai muku qari, kuma ambaton Allah shine mafi girma, kuma lallai Allah ya san abinda kuke aikatawa.
,,,          ,,,          ,,,
,,,          ,,,          ,,,


TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان)

TSAWATARWA DAGA SHAN TABAR SIGARI (التحذير من شرب الدخان) Na Shehun Malami Abdul’aziz dan Abdullahi bn Baaz Allah ya yi masa rahama...